Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
Published: 12th, April 2025 GMT
’Yan sanda sun kama wani magidanci bisa zargin ya ɗirka wa ’yar cikinsa mai shekara 17 ciki a yankin Kariya da ke Ƙaramar Hukumar Ganjiwa a Jihar Bauchi.
Kakakin ’yan sandan jihar, Ahmed Wakil ya ce an kama mutumin mai shekaru 50 ne bayan samun ƙara cewa ya yi wa ’yar tasa fyaɗe fiye da sau ɗaya a ɗakinsa.
Wakil ya ce a yayin bincike magidancin ya amsa cewa ya sha zakke wa ’yar tasa a gida, kuma bayan an yi mata gwaji a asibiti aka tabbatar cewa tana ɗauke da ciki wata uku.
Ya ce yarinyar ta shaida wa masu bincike cewa a lokacin da mahaifiyarta ta yi tafiya zuwa garin iyayenta a Ƙaramar Hukumar Ningi da ke jihar ne mahaifin nata ya yi amfani da damar ya riƙa lalata da ita.
An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi ’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a KatsinaBayan dawowar mahaifiyar ce ta lura da alamun juna biyu a tare da ’yar, kuma bayan ta titsiye ta, ta shaida mata cewa mahaifinta ne ya yi mata cikin.
Wakil ya ce rundunar tana ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin, kuma kwamishinan ’yan sandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gurfanar da wanda ake zargin a kotu da zarar an kammala bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
Kwamitin wucin-gadi na Majalisar Wakilan Nijeriya wanda aka ɗora wa alhakin kula da harkokin gudanar da mulki a Jihar Ribas, ya gayyaci gwamnan riƙon jihar, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas.
Wannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Majalisar Wakilan, Akin Rotimi ya fitar a ranar Laraba.
An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a FilatoRotimi ya ce gayyatar na zuwa ne bayan ƙaddamar da kwamitin da Shugaban Majalisar Abbas Tajudeen ya yi a ranar Talata.
Ya ce gayyatar za ta bai wa kwamitin damar yin bita kan yadda al’amura ke gudana tun bayan kama ragamar aiki da Ibas ya yi a matsayin gwamnan riƙo a jihar ta Ribas.
Gayyatar wadda tuni ake aike da ita a hukumance, ta yi daidai da wasu tanade-tanade na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, inda ta buƙaci Ibas ya bayyana a gaban kwamitin da misalin ƙarfe 4 na maraicen ranar Alhamis, 17 ga watan Afrilun 2025.
A jiya Talata ce Majalisar Wakilan ta kafa tare da rantsar da kwamitin da zai kula da harkokin mulki a Jihar Ribas.
Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas ya ce kwamitin na wucin gadi mai mamba 21 zai yi aiki kai-tsaye da gwamnan riƙo “kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya tanada.”
Majalisar ta kafa kwamatin ne bayan Shugaba Bola Tinubu ya saka dokar ta-ɓaci wadda ta dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar saboda abin da ya kira “rushewar doka da oda.”
Har yanzu dai ’yan adawa na zargin cewa Tinubu ya kafa dokar ne saboda rikicin siyasar da gwamnan na jam’’yyar PDP mai adawa yake yi da Ministan Abuja, Nyesom Wike, wanda ke ɗasawa da gwamnatin Tinubu ta APC.