Leadership News Hausa:
2025-05-01@04:44:58 GMT

Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13

Published: 11th, April 2025 GMT

Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13

Kudin biyan bashin cikin gida na shekarar 2024 ya kai naira tiriliyan 5.97, wanda hakan ke nuna karin kashi 14.15 cikin 100 daga naira tiriliyan 5.23 da aka samu a shekarar 2023. Karuwar ana danganta shi da karuwar kudin ruwa da karin lamuni na cikin gida.

Nijeriya dai ta kashe dala biliyan 4.66 (kwatankwacin naira tiriliyan 7.

15 kan farashin canjin naira 1,535.32/$1), wanda hakan ya nuna karuwar kashi 167 cikin 100 daga naira tiriliyan 2.57 da aka samu a shekarar 2023.

Yawan kudin biyan basussuka na waje yana da nasaba da hauhawar farashin ruwa a duniya da kuma faduwar darajar naira, lamarin da ya sa bashin dala ya yi tsada wajen aiki.

Duk da yawan kudin basukan da ke kan Nijeriya, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da ciwo basuka kadan ta yi amfani da su cikin hanyoyin da suka dace.

Shettima ya bayyana haka ne a karshen makon da ya gabata a Abuja, yayin wani taron da kungiyar akanta ta kasa ta kasa da kuma cibiyar harajin ta Nijeriya ta shirya.

Mataimakin shugaban kasar, wanda ya samu wakilcin mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki, Dakta Tope Fasua, ya bayyana cewa sannu a hankali ana sake fasalin tsarin karbar basussukan da gwamnati ke yi domin rage bashin.

Ya kuma bayyana cewa, duk da rancen da aka karbo a baya-bayan nan da ya jawo cece-kuce, yanzu Nijeriya na kan hanyar karbar rancen kadan tare da kokarin rage gibin kasafin kudaden da ake fuskanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya naira tiriliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Mista Mark Joseph Carney murna bisa zaɓensa a matsayin Firaiminista na 24 na ƙasar Kanada, bayan nasarar jam’iyyar Liberal a zaɓen majalisar dokokin da aka kammala kwanan nan.

 

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana zaman Carney a wannan matsayi a matsayin wani muhimmin ci gaba, musamman a wannan lokaci da Kanada ke bukatar gogaggen shugaba domin fuskantar ƙalubale da dama.

 

Carney, wanda fitaccen masani ne a fannin tattalin arziki, ya taba rike mukamin Gwamnan Babban Bankin Kanada daga shekarar 2008 zuwa 2013, sannan ya ci gaba da zama Gwamnan Babban Bankin Ingila daga 2013 zuwa 2020.

 

Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwar cewa ƙwarewar sabon shugaban Kanada a fannin kuɗi da shugabanci za ta taka muhimmiyar rawa wajen gina makomar ƙasar. Haka kuma, ya sake jaddada kudirin Najeriya na ƙarfafa dangantakar diflomasiyya da Kanada, musamman a fannonin ilimi, sauyin yanayi da hijira.

 

Shugaban Najeriya ya ƙara da cewa yana fatan kafa kyakkyawan hadin gwiwa da gwamnatin Carney, yayin da ya nuna godiyarsa ga kyakkyawar alakar da aka kula a tsakaninsu  a zamanin tsohon Firayim Minista, Justin Trudeau.

 

Bello Wakili

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai