Aminiya:
2025-07-09@07:57:34 GMT

An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi 

Published: 12th, April 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta ce, tana gudanar da bincike kan wani dukan kawo wuƙa da wasu matasa suka yi wa waɗansu mutane su biyu da ake zargi da satar kare a unguwar Lushi da ke cikin garin Bauchi.

Dukan da ya yi sanadin rasa ran ɗaya daga cikinsu mai suna Peter.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya sanar da haka ga manema labarai a Bauchi, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Larabar da ta gabata kan wani mutum mai suna Peter a ranar 9 ga Afrilu, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na dare.

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Wakil ya ce waɗanda ake zargi Dokagk Danladi mai shekara 38 da kuma Peter matasan sun musu duka ne sakamakon zargin da ake musu.

Ya ce, “Dokagk ya samu munanan raunuka da suka haɗa da raunukan sara da adda a kansa, kuma tuni aka kai shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) da ke Bauchi domin kula da lafiyarsa, an gano abokin nasa Peter, wanda har yanzu ba a san sunan babansa ba, a wurin da lamarin ya faru, abin takaici ma’aikatan lafiya sun bayyana cewa shi peter ya mutu.”

A halin yanzu ana gudanar da bincike.  Rundunar tana aiki tuƙuru don ganin an gudanar da cikakken bincike kan wannan lamari, tare da maida hankali wajen zaƙulo duk waɗanda ke da hannu a lamarin.

Wakil ya ce babban Jami’in  ’yan sanda da ke kula da shiyyar Yalwa (DPO) yana jagorantar tawagar masu binciken waɗanda suka ziyarci wurin da laifin da ya faru don tattara shaida da samun cikakken bayanai kan lamarin  .

Kakakin rundunar ’yan sandan ya ce, Kwamishinan ’yan sandan, Sani-Omolori Aliyu ya bayyana wannan aika-aika a matsayin “wata ɓarna da kuma illa ga tsarin dokokin ƙasarmu”.

“Ya kuma gargaɗi ’yan asalin Jihar Bauchi cewa, a ƙarƙashin shugabancinsa rundunar ba za ta lamunci duk wani mutum da ke ɗaukar doka a hannunsu ta hanyar cutar da waɗanda ake zargi da aikata laifukan da suka saɓa wa doka ba.

“Ya ƙara jaddada cewa, babu wani mutum da ke da hurumin mu’amala da wanda ake tuhuma ta hanyar da ba ta dace ba, kuma hakan ba daidai ba ne ga kowa ya ɗauki nauyin aiwatar da doka.  Ya kamata a gaggauta miƙa waɗanda ake zargi da aikata laifin da ake tuhuma ga ‘yan sanda ko hukumomin da abin ya shafa da ke da alhakin bincike da gurfanar da su a gaban kotu.”

Kwamishinan ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu yayin da ake ci gaba da bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda a Bauchi Yan Sanda satar kare da ake zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Mutun 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano

Aƙalla mutum 21 ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babban titin Zariya zuwa Kano, kamar yadda Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), ta tabbatar.

Hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 8:23 na safe a unguwar Kasuwar Dogo da ke yankin Dakatsalle.

Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe

Hatsarin ya rutsa da wata babbar mota ƙirar DAF mai lambar GWL 422 ZE da kuma motar ɗaukar fasinjoji ƙirar Toyota Hummer mai lambar KMC 171 YM.

FRSC, ta ce bincike ya nuna cewa direban motar fasinjojin ne ya karya doka ta hanyar bin hanyar da ba ta dace ba, wanda hakan ya sa suka yi karo da babbar motar.

Bayan aukuwar hatsarin, motocin biyu sun kama da wuta, inda mutane da dama suka ƙone ƙurmus.

Kwamandan FRSC na Kano, MB Bature, ya ce jami’ansu sun isa wajen cikin gaggawa bayan samun rahoto.

Sun kuma kira ma’aikatan kashe gobara na jihar da na tarayya domin kashe gobarar da kuma ceto waɗanda hatsarin ya rutsa da su.

Mai magana da yawun FRSC, Abdullahi Labaran, ya ce: “Mutum 24 ne hatsarin ya rutsa da su. Abin takaici, 21 sun rasu, yayin da uku suka jikkata.”

Gawarwakin da suka ƙone an kai su ɗakin ajiye gawa na Asibitin Nassarawa da ke Kano, yayin da waɗanda suka jikkata ke samun kulawa a Asibitin Gwamnati da ke Garun Malam.

Bayan haka, jami’an FRSC tare da taimakon ’yan sanda sun ɗauke motocin da suka tare hanya domin sauƙaƙa zirga-zirgar ababen hawa a titin.

Kwamanda Bature, ya bayyana alhininsa kan wannan mummunan lamari, tare da miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu.

Ya kuma yi wa waɗanda suka jikkata addu’ar samun sauƙi.

Ya kuma yi amfani da wannan dama wajen jan hankalin direbobi su guji karya doka; kamar bin hanya ba daidai ba da tuƙin ganganci, wanda hakan ke haddasa haɗura.

“Wannan lamari abin takaici ne wanda ke nuna muhimmancin bin ƙa’idojin hanya. Mafi yawan haɗura za a iya kauce musu idan direbobi za su kiyaye doka,” in ji Bature.

Ya kuma buƙaci direbobi, musamman na motocin haya, da su guji gudu fiye da ƙima da ganganci a hanya, wanda a cewarsa shi ne babban dalilin da ke haddasa haɗura da asarar rayuka.

Ga hotunan yadda hatsarin ya auku:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, sun Jikkata 4 a Borno
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  •  Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda
  • Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano
  • Mutun 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano