Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
Published: 15th, June 2025 GMT
Iran ta sanar da soke zaman tattaunawa da ya kamata ta yi da Amurka kan batun nikiliyarta a Oman yau Lahadi saka makon hare-haren da Isra’ila ta kai mata a ranar Juma’a.
Bayanai sun ce a wannan Lahadin ce ya kamata a gudanar da ganawa ta shida tsakanin wakilan Amurka da na Iran a birnin Musqat na Oman.
Sai dai kakakin Ministan harkokin wajen Iran, Esmaeil Baqaei ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, Amurka ta nuna fuska biyu, inda a gefe guda take tattaunawar cimma masalahar jingine ƙera nukiliya da Iran, amma a ɗaya gefen kuma ta goyi bayan harin da Isra’ila ta kai mata.
Iran ta zargi Amurka da goyon bayan harin da Isra’ila ta kai mata, sannan kuma ta ce tattaunawar yarjejeniyar dakatar da ƙera makamin ƙare dangi na nukiliya da take yi da Amurkar ba ta da wani amfani.
A nasa ɓangaren, Ministan harakokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce babu buƙatar ci gaba da tattaunawa da aka faro tsakiyar watan Afirilun wannan shekara lura da harin dabbanci da Isra’ila ta kai mata.
Kafofin yaɗa labarai da dama a Iran sun shaida cewa guda daga cikin masu baiwa jagoran addinin musluncin Iran ayatoAllah Ali Khamenei kuma mai taka muhimmiyar rawa a tattaunawar, Ali Shamkhani, na daga cikin waɗanda su ka ji rauni a hare-haren na Isra’ila.
Tun farko Isra’ila ce ta fara kai wa Iran hari kan cibiyoyin nukiliyarta tare da halaka manyan hafsoshin tsaronta, cikin daren Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a, kuma ta ci gaba da kai farmaki da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, mafarin buɗe kofar wani sabon rikici a tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna adawa da juna tsawon shekaru.
Harin ramuwar gayya da Iran ta kai wa Isra’ila da safiyar Asabar ya halaka mutane uku, tare da jikkata wasu da dama a biranen Jerusalem da Tel Aviv, inda hukumomin Isra’ila ke ci gaba da gargaɗin ‘yan kasar su nemi mafaka.
A wani jawabi da jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya gabatarwa al’ummar kasar ranar Juma’a, ya ce ba za su saurara wa Isra’ila ba sakamakon munin abin da ta aikata musu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iran Isra ila nukiliya da Isra ila ta kai mata
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
Gwamnatin Jigawa ta amince da sabon tsarin ka’idojin aiki domin aiwatar da shirin kula da lafiyar mata masu juna biyu, da jarirai da ƙananan yara kyauta a cibiyoyin lafiya na jihar.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana haka bayan zaman majalisar zartarwa da aka gudanar a gidan gwamnati Dutse.
Ya ce ka’idojin za su taimaka wajen inganta nagartar hidima, fayyace karewar ma’aikata, da kuma tabbatar da gaskiya, da bin doka da tsari a asibitoci.
Kwamishinan ya ƙara da cewa matakin ya dace da manufar gwamnatin jihar na rage mace-macen mata da yara da kuma tabbatar da samun ingantacciyar kulawa ga kowa.
Ya ce za a fara aiwatar da tsarin nan take, tare da horas da shugabannin asibitoci da cibiyoyin lafiya na ƙananan hukumomi domin cimma nasarar shirin .
Usman Muhammad Zaria
—
Kana so in ƙara ɗan salo na labarin jarida (irin rubutun kafafen yaɗa labarai) ko a barshi haka cikin sauƙin bayani?