Ofishin kwamitin kolin JKS da na majalisar gudanarwar kasar Sin, sun sanar da kaddamar da sabon shiri game da tsare-tsaren musamman na bunkasa sayayya a kasar Sin, a gabar da kasar wadda ita ce ta biyu a karfin tattalin arziki a duniya ke kara karkata ga mayar da kasuwannin gida ginshiki, kuma babban karfi na ingiza ci gaban tattalin arzikinta.

Shirin wanda ofisoshin biyu suka yi hadakar sanar da shi a jiya Lahadi, ya kunshi dabarun bunkasa sayayya, da ingiza bukatun cikin gida a dukkanin sassa, da fadada karfin sayayya ta hanyar kara yawan kudaden shiga, da rage nauyin da al’umma ke fuskanta ta fuskar bukatun kudi.

Kazalika, shirin na fatan ingiza karin bukatu ta hanyar samar da ingantattun hidimomin gabatar da hajoji, da kara kyautata muhallin sayayya ta hanyar karfafa gwiwar al’umma don yin sayayya, da magance kalubale dake yiwa al’umma tarnaki wajen sayayya.

Bugu da kari, shirin wanda aka tsara zuwa manyan sassa 8, zai mamaye dukkanin sassa ta hanyar magance mataloli, kamar wadanda ke dakile karuwar kudaden shiga, da masu tarnaki ga ingancin hidimomi, da daga matsayin sayayyar abubuwa da ake mallaka ta manyan tikiti, da kara inganta yanayin muhallin sayayya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC

Ƙungiyar matasan jam’iyyar APC reshen Jihar Kano ta ce guguwar sauyin sheƙa ta jiga-jigan ’yan siyasa da ke ficewa daga jam’iyyar NNPP alama ce da ke nuna cewa tasirin tsohon Gwamnan Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso a siyasance na ƙara disashewa.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar matasan ta KASASCO ta fitar a ranar Talata, ta ce a halin yanzu jam’iyyar APC ba ta buƙatar dawowar Kwankwaso cikinta saboda tasirinsa a siyasance na ci gaba da gushewa.

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno

Darekta Janar na KASASCO, Kwamared Yahaya Usman Kabo, ya ce jam’iyyar APC a ƙarƙashin jagorancin Abdullahi Abbas ta yi tsayuwar daka da kafa tubalin samun nasara a Zaɓen 2027 da ke tafe, la’akari da cewa tana da Sanatoci biyu da kuma wakilci mai ƙarfi a matakin jiha da tarayya.

Ya bayyana cewa guguwar sauyin sheƙa da ke kaɗawa a jam’iyyar NNPP na da nasaba da tasirin jiga-jigan jam’iyyar da suka tsaya kai da fata wajen tabbatar da nasararta a Zaɓen 2023.

Sai dai ya ce a yanzu jiga-jigan jam’iyyar ta NNPP na ficewa daga cikinta zuwa APC saboda zargin rashin adalci da mayar da su saniyar ware da ’yan Kwankwasiyya suka yi.

Aminiya ta ruwaito cewa daga cikin jiga-jigan NNPP da suka sauya sheƙa zuwa APC a bayan nan akwai Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila da Kabiru Alhassan Rurum da Abdullahi Sani Rogo da Zubairu Hamza Massu.

Akwai kuma Abbas Sani Abbas da Baffa Bichi da kuma Sha’aban Ibrahim Sharada.

Ya ce “sauyin sheƙar waɗannan jiga-jigan ’yan siyasa ta karya garkuwar jam’iyyar a Kano. Saboda haka yanzu APC ta warware duk wasu matsalolin cikin gida da take fuskanta domin tabbatar da nasarar a 2027.”

APC ta ce tana da yaƙinin samun nasara a zaɓen da take tafe wanda take fatan bai wa Shugaba Bola Tinubu ƙuri’u miliyan biyu a Jihar Kano.

Sai dai ta ce dawowar Kwankwaso jam’iyyar babu abin da zai haifar sai kawo ruɗani a cikinta.

“A yanzu Kwankwaso ba shi da wani tasiri a siyasance, shi ya sa yake neman mafaka da babu inda zai same ta face a jam’iyyar APC.

“Sai dai yana da kyau ya fahimci cewa APC ba wuri ba ne na samun mafaka kuma ba ta buƙatar irinsu [Kwankwaso] da babu abin da za su kawo wa jam’iyyar face ruɗani.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Cinikayyar Hidima Ta Kasar Sin Ta Matukar Bunkasa A Rubu’in Farko Na Nana
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Kasar Sin Ta Kyautata Tsarin Mayar Da Kudin Haraji Domin Karfafa Gwiwar Yin sayayya A Kasar