Sin Ta Kaddamar Da Sabon Shiri Kan Tsare-tsaren Musamman Don Bunkasa Sayayya
Published: 17th, March 2025 GMT
Ofishin kwamitin kolin JKS da na majalisar gudanarwar kasar Sin, sun sanar da kaddamar da sabon shiri game da tsare-tsaren musamman na bunkasa sayayya a kasar Sin, a gabar da kasar wadda ita ce ta biyu a karfin tattalin arziki a duniya ke kara karkata ga mayar da kasuwannin gida ginshiki, kuma babban karfi na ingiza ci gaban tattalin arzikinta.
Shirin wanda ofisoshin biyu suka yi hadakar sanar da shi a jiya Lahadi, ya kunshi dabarun bunkasa sayayya, da ingiza bukatun cikin gida a dukkanin sassa, da fadada karfin sayayya ta hanyar kara yawan kudaden shiga, da rage nauyin da al’umma ke fuskanta ta fuskar bukatun kudi.
Kazalika, shirin na fatan ingiza karin bukatu ta hanyar samar da ingantattun hidimomin gabatar da hajoji, da kara kyautata muhallin sayayya ta hanyar karfafa gwiwar al’umma don yin sayayya, da magance kalubale dake yiwa al’umma tarnaki wajen sayayya.
Bugu da kari, shirin wanda aka tsara zuwa manyan sassa 8, zai mamaye dukkanin sassa ta hanyar magance mataloli, kamar wadanda ke dakile karuwar kudaden shiga, da masu tarnaki ga ingancin hidimomi, da daga matsayin sayayyar abubuwa da ake mallaka ta manyan tikiti, da kara inganta yanayin muhallin sayayya. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.
Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.
An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.
“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.
Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.
Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.
Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.
An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.
Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.