Leadership News Hausa:
2025-12-01@17:05:15 GMT

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

Published: 17th, October 2025 GMT

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

Baya ga yi masu afuwa, Shuagaba Tinubu, ya kuma karama su da lambar yabo ta kasa.

‘Yan Ogonin su tara, sun dai fuskanci shari’a ne, bisa zarginsu da kitsa kisan sarakunan Ogoni Albert Badey, Edward Kobani, Theophilus Orage da kuma Samuel Orage.

Kotu ta tuhumi ‘yan Ogonin su tara, ta kuma yanke masu hukuncin rataya a ranar 10 ga watan Numambar 1995.

Hukucin na Kotun, a wancan lokacin, ya haifar da hatsaniya tare da yin suka daga bangaren manyan shugabannin kasasshen duniya, daidaikun mutane da sauran kungiyoyi, musaman duba da cewa, an yanke masu hukuncin ne, a lokacin da ‘yan kasar ke nuna tsanar mulkin soji, biyo bayan soke zaben shugaban kasa, da ake da yakinin an yi sahihin zabe ne.

Sai dai, masu sharhi a fagaen siyasa na ganin Tinubu ya yi masu wannan afuwar ce, da wata manufa, musamman ganin yadda afuwar ta kasance, tare da karrama su da lambar yabo ta kasa.

Amma idan aka yi dubi da yunkurin da Tinubu ke ci gaba da yi na tabbatar da sasanci a daukacin mazauna yankunan kasar komai kankancin da yanki yake dashi, musamman wadanda suka ganin, an mayar da shu, Saniyar ware, ko kuma an manta da su, wannan kokarin na sa na son hada kan kasar, hakan ya zama wajibi, suma ‘yan Oginin hudu, hakan ya sa Tinubu, ya sanya ‘yan Ogoni hudu, a cikin jeren wadanda aka yiwa afuwar

Domin idan har ba sanya su cikin jeren wadanda suka suka ci wannan gajiyar ta afuwar ba, hakan zai zama tamkar an yi tuya ne, an manta da Albasa, inda yin wannan afuwar, za ta kara tabbatar da zaman lafiya mai dorewa, a yankin.

Wannan Jaridar na goyon bayan duk wani abu, da ya shafi yin adalci da kuma bai wa, kowanne bangaren na kasar hakkainsa.

A saboda hakan, muna jinjinawa Shugaba Tinubu kan yin wannan afuwar ga ‘yan Oginin su hud, wanda wannan matakin ya bude wani sabon babain tarihi ga turbar makomar mulkin Dimokiradiyyar kasar.

Alal misali, a lokacin tsohuwar gwamnatin mulkin soji ta Janar Yakubu Gowon mai murabus, bayan karshen yakin basa na shekarar 1970, ya yi wadanda suka taka muhimmiyar raywa a yakin afuwa.

Bugu da kari, a lokacin tshowar gwamnatin farar hula ta marigayi tsohon Shugaban kasa Shehu Shagari, ya yiwa Dim Chukwuemeka Odumegwu Ojukwu, afuwa ya kuma rufe kundinsa na aikata jan ragamar yakin basasan, wanda hakan ya sa samu damar dawo cikin kasar bayan barin kasar domin neman mafakar siyasa.

Batun na Ogoni wani abu ne da za a iya cewa, cike yake da nuna karfin kwanji a tsakanin wasu manyan masu fada aji, a yankin, inda matsalar ta kuma haifar kusan kawo karshen rayuwar manyan jiga-jigan da ke a yankin, musamman ganin yadda wasu mayan yankin, a wancan lokacin, suka rinka karkatar da dimbin arzikin, da ya kamata mazauna yankin, su mafana da su, musamman wajen magance dagwalon danyen mai da ke lalata muhalli a yankin.

Tataburzar wadda ta auku a lokacin tsohuwar gwamnatin mulkin siji ta marigayi Janar Sani Abacha, ta samu nasarar cin lagon ‘yan yankin da suka yi uwa suka kuma yi makarbiya wajen siyasantar da batun.

Wasu masu kare muradun siyasa a wancan lokacin, sun alakanta kisan da gwamnatin Abacha ta yiwa ‘yan Ogoni su tara, a matsayin abinda ya sabawa mulkin Dimokiradiyya.

Koma dai menene, daukacin batun ya bayyana a zahiri, irin kalubalen da yankin ke fuskanta a wancan lokacin, na gurbacewar muhalli a yankin.

Sharhin wannan Jaridar kan batun, ba wai wata manufa ce, ta dora laifin kan wani bangare ba, domin kuwa an yi rubuce-rubuce da dama na goyon baya da kuma na yin suka, domin a yanzu, duk wani yunkuri na nuna jayya hakan zai iya zama, tamkar fama wani Gyambo ne.

A nan, muna kira ga Shugaba Tinubu da kai daukin tallafawa rayuwar wadanan ‘yan Ogonin hudu, domin kuwa afuwar da kuma bayar da lambar karramar ga ‘yan Ogonin tara, ba su wadatar ba, ganin cewa, sauran hudu da ba a sanya su a cikin ba, hakan zai iya ci gaba da jefa tamtama.

Suma ‘yan Oginin hudu, ‘yan Nijeriya ne, kamar kowa duba da yadda suka sadaukar da rayukansu, domin dorewar yankinsu

Har dai zuwa yau, ba a iya gano gawarwakin ‘yan Ogonin tar aba, inda su kuma ‘yan Ognin hudu suka rasa na su rayukan a cikin wani irin yanayi.

A bisa wadannan dalilan, muna sake nanata kiran mu da tattausar murya ga Shugaba Tinubu da sake yin bibiya kan batun na ‘yan Ogoni hudu, musamman domin tabbatarda zaman lafiya mai dorewa a yankin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayinmu Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai October 10, 2025 Ra'ayinmu Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan September 7, 2025 Ra'ayinmu A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya August 29, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a wancan lokacin

এছাড়াও পড়ুন:

Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban

Asibitin Kula da masu lalurar kwakwalwa da ke Kaduna na Jagorantar Sauye-Sauren Lafiyar ƙwaƙwalwa a Arewacin Najeriya — Farfesa Aishatu Armiya’u Ta Bayyana Muhimman Nasarori a Shugabanci da Ayyuka da Hadin Gwiwa

Shugabar gudanarwa kuma daraktar lafiya ta Asibitin kula da masu lalurar ƙwaƙwalwa dake Kaduna, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u, ta tabbatar da kudirin asibitin na ci gaba da jagorantar gyaran tsarin kula da lafiyar kwakwalwa a Arewa, inda ta ce an samu gagarumin ci gaba wajen fafutukar manufofi, kara yawan ayyuka, da karfafa hadin gwiwa tsakanin sassa daban-daban a cikin shekaru uku da suka gabata.

Farfesa Armiya’u ta bayyana cewa horon da ta samu a shirye-shiryen shugabancin harkokin lafiya na Africa ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta salon shugabancinta da kare muradun lafiyar kwakwalwa, da kuma gina ƙwarewa a fannin.

Ta bayyana shirin a matsayin ginshiƙi wajen karfafa mata kwarewar tsara manufofi da aiwatar da gyare-gyaren tsarin lafiya.

Sauya Fasalin Babban Asibitin na kasa dake Kaduna

A matsayinta na shugabar daya daga cikin manyan asibitocin kula da lafiyar kwakwalwa guda goma na tarayyar Najeriya, Farfesa Armiya’u ta jagoranci sauye-sauren da suka mayar da Asibitin Kaduna cibiyar kula da lafiya ta tunani da jiki, bincike, da horas da kwararru a hanya mai dacewa da al’adu.

A karkashin jagorancinta, asibitin ya kafa dimbin yarjejeniyar hadin gwiwa da kungiyoyin cikin gida da na waje don bunkasa lafiyar kwakwalwa ga al’umma.

Daya daga cikin manyan hadin gwiwar ita ce wadda ake yi da Hukumar Rigakafin Shan Miyagun Kwayoyi da Kula da Lafiyar ƙwaƙwalwa ta Jihar Kaduna wadda ta taimaka wajen samun ci gaba sosai a bangaren manufofi da ayyuka a jihar.

Manyan Nasarorin Manufofi a Jihar Kaduna

Ta hanyar hadin gwiwa da KADSAMHSA, asibitin ya bada goyon bayan fasaha wajen tsara dokoki da tsarin aiki da ake amfani da su wajen sauya fasalin kula da lafiyar kwakwalwa a fadin jihar. Muhimman nasarorin sun hada da:

Sanya magungunan psychotropic a cikin Jerin Muhimman Magungunan Jihar Kaduna na 2025, wanda zai tabbatar da samunsu a cibiyoyin lafiya na matakin farko da na biyu.

Taimakawa wajen tabbatar da dokar Lafiyar ƙwaƙwalwa ta Jihar Kaduna, da amincewa da wata manufa da ke haɗa lafiyar kwakwalwa da cibiyoyin kiwon lafiya na al’umma.

Shirin horaswa da ya kara yawan aikace-aikacensu a fadin jihar, wanda ya bai wa ma’aikatan lafiya 165 horo a manyan asibitoci 15, ciki har da masu kula da samari masu dauke da cutar HIV.

Ta kuma ce asibitin yanzu yana da tsofaffin dalibai 10 na Africa CDC Mental Health Leadership Programme — waɗanda aka horar a Ibadan, Nairobi, da Cairo — kuma kowannensu yana jagorantar muhimman ayyukan gyara.

Inganta Walwalar Ma’aikata da Ingancin Ayyuka

Farfesa Armiya’u ta jaddada cewa jin dadin ma’aikata na daga cikin manyan abubuwan fifiko, inda aka kirkiro sababbin shirye-shiryen da ke inganta lafiyar jiki, tunani da zamantakewa.

Wadannan sun hada da makon lafiya na kowane kwata, wasanni, tarukan zamantakewa, da ingantaccen tsarin inshorar lafiya.

Asibitin ya kuma hade kula da lafiyar jiki cikin ayyukan lafiyar kwakwalwa, tare da kyautata muhalli domin karfafawa da rage wariya.

Wadannan matakai sun kai ga samun babban gamsuwa daga marasa lafiya, inda sama da kashi 90 cikin dari suka bayyana jin dadi da kulawar da suka samu.

Fadada Ayyuka Ta Hanyar Karin Hadin Gwiwa

Asibitin na kara fadada tasirinsa ta hanyar aiki tare da rundunar sojoji, cibiyoyin ilimi, kungiyoyin farar hula, da sauran abokan hulda.

Wadannan hadin gwiwar na taimakawa wajen ba da dama ga karin al’umma su samu kula da lafiyar kwakwalwa a Arewa, tare da karfafa kula da marasa lafiya a cikin al’umma.

Shirye-Shiryen Gaba: Kirkire-Kirkire da Kula da Al’umma

Dangane da makomar asibitin, Farfesa Armiya’u ta bayyana cewa za a kara karfafa tsarin kula da lafiyar kwakwalwa na al’umma, habaka bincike da kirkire-kirkire, fadada amfani da kayan aikin lafiyar kwakwalwa na dijital, da gina karfin ma’aikatan lafiya domin biyan bukatun al’umma da ke ta ci gaba da sauyawa.

Ta jaddada himmar gina tsarin lafiyar kwakwalwa mai tausayi, wanda ba ya takaituwa ga manyan cibiyoyi kawai, kuma ya dace da al’adu — wanda za a iya yada shi a fadin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
  • DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali
  • Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban
  • China Ta Gargadi Amurka Akan Batun Yakar Kasar Venezuela