Rahotanni na nuna cewa akwai yiwuwar Shugaban Kasa Bola Tinubu ya cire wasu sunaye daga jerin wadanda ya yi wa afuwa bayan cece-kucen da hakan ya jawo.

Hakan dai ya biyo bayan ci gaba sukar lamirin hakan da jama’a ke yi, musammam kan saka wasu rikakkun masu laifi da kotu ta yanke wa hukunci daban-daban.

Saudiyya ta zaftare wa Najeriya guraban Aikin Hajji da sama da kujeru 28,000 ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara

Afuwar shugaban kasa da ake bayarwa a lokutan bukukuwan ƙasa, ana yin ta ne don rage cunkoso a gidajen yari da kuma ƙarfafa sulhu da haɗin kai.

Sanarwar fadar shugaban kasa ta ce an yanke shawarar ne bisa shawarwarin Kwamitin Shawara na Shugaban Ƙasa kan Afuwa, wanda Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi ke jagoranta.

Sai dai wannan lamari ya sake tayar da cece-kuce kan gaskiya da sahihancin tsarin afuwar Najeriya.

Amma a ranar Alhamis, Ministan na shari’a ya ce afuwar da shugaban kasa ya sanar ba a kammala tantance ta ba, kuma har yanzu akwai sauran matakan da ba a kammala cikawa ba.

Cece-kuce na ci gaba da tasowa kan wasu sunaye da aka haɗa a ciki, inda hukumar EFCC, ICPC da NDLEA da sauran hukumomin tsaro suka fara kokarin dakatar da sakin wasu daga cikin waɗanda ke cikin sunayen.

A taron Majalisar Koli da aka gudanar a ranar 9 ga Oktoba, 2025, fadar shugaban kasa ta shelanta sunayen mutum 175 da aka yi wa afuwar, ciki har da masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, masu laifukan ofis, masu laifukan miyagun ƙwayoyi, Manjo-Janar Mamman Vatsa, Farfesa Magaji Garba, Ken Saro-Wiwa, mutanen Ogoni, Maryam Sanda da ma wasu da dama.

Yayin da sunayen wasu ’yan siyasa kamar Herbert Macaulay da Farouk Lawan ba su haifar da cece-kuce ba, haɗa sunayen masu laifukan tashin hankali da karya doka ya jawo fushi daga jama’a.

Daya daga cikin sunayen da suka jawo cece-kuce shi ne Maryam Sanda, wacce aka yanke wa hukuncin kisa a 2017 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello.

Yayin da wasu daga cikin iyalan marigayin suka ƙi amincewa da afuwar, Alhaji Bello Isa (mahaifin mamacin) da Alhaji Garba Sanda (mahaifin Maryam) sun gudanar da taron manema labarai don karɓar afuwar ta shugaban kasa.

Shugaban kasa ya kuma yi wa Major S. Alabi Akubo afuwa, wanda aka yanke wa hukuncin daurin rai da rai kan mallakar makamai ba bisa ka’ida ba, da kuma Kelvin Prosper Oniarah, wanda aka danganta da hare-haren garkuwa da mutane a jihohin Delta, Edo, Ribas, Abia, Binuwai da Oyo, inda aka gano sansanoninsa na tsare mutane a Warri, Kokori, Ugbokolo, Benin City da Aba.

Kazalika, sunayen waɗanda aka yanke wa hukunci kan kashe jami’an tsaro, safarar miyagun ƙwayoyi, da satar kuɗi, da sauransu, sun jawo tambaya daga jama’a.

Rahotanni sun nuna cewa wannan cece-kuce ya sa fadar shugaban kasa ta fara nazarin sake duba tsarin afuwa, tare da yiwuwar cire sunayen da suka jawo suka daga jama’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Afuwa Maryam Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda

Fadar  gwamnatin kasar Iraki ta sanar da cewa ba ta masaniya akan yadda aka shigar da sunayen Ansarullah na Yemen da kuma Hizbullah ta kasar Lebanon a cikin jerin sunayen kungiyoyin ‘Yan ta’adda da aka rike kudadensu dake bankunan kasar.

Bayanin fadar gwamnatin kasar ta Iraki ya kuma kara da cewa; Matakai irin wadannan da ake dauka a kasar ba a aike wa da su zuwa fadar shugaban kasa,abinda ake aikewa fadar shi ne dokokin da majalisar dokokin kasar ta yi, domin a sake tantancewa da kuma amincewa.”

Haka nan kuma sanarwar ta ce; wasu daga cikin abubuwan da ake aikewa fadar mulkin kasar sun hada da tsare-tsaren fadar shugaban kasa,amma abinda ya shafi matakan majalisar ministoci, da na kwamitin dake dakatar da kudaden ‘yan ta’adda da na kwamitin da yake sa ido akan masu wanke kudaden haram, ba a aikewa fadar gwamatin kasar.”

A karshe bayanin ya ce, fadar gwamantin kasar ba ta da wata masaniya akan matakan da aka dauka na bayyana Ansrullah da Hizbullah a matsayin kungiyoyin ‘yan ta’adda tare da daukar matakan hana amfani da kudadensu a cikin bankunan kasar ta Iraki.

Sanarawar da aka yi a kasqar Iraki a shekarun jiya Alhamis na cewa an hana wasu kungiyoyi da su ka hada “Isis, alka’ida, Ansarullah da kuma Hizbullah, amfani da bankunan kasar domin hada-hadar kudade, ya tayar da kura a cikin da wajen kasar. Mutane sun fito kan titutan kasar ta Iraki domin yin tir da wannan sanarwa.

Sai dai daga baya gwamantin kasar ta janye wannan sanarwa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa December 6, 2025 Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Trump Ya Yabawa Rwanda Da Kongo DMK Kan Sulhuntawa A Yakin Gabancin Kongo December 5, 2025 Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu December 5, 2025 Shin Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump? December 5, 2025 Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump December 5, 2025 Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Taimaka Wa Laifukan Isra’ila A Kan Falasdinawa December 5, 2025 Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania December 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Nigeria: Har Yanzu Da Akwai Daliban Makaranta 250 Da Suke Hannun Masu Garkuwa Da Su
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru