Mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa, taron goron gayyata ne na kafa Nijeriya a matsayin cibiyar samar da makamashi tare da sabuntawa a Afirka, sannan kuma sauyin da aka samu na makamashi Nijeriya, ya bayar da damar zuba jari na sama da dala biliyan 410, daga tsakanin yanzu zuwa shekarar 2060.

Ya kara da cewa, “Daga cikin wannan, ana kuma bukatar sama da Naira biliyan 23, domin fadada hanyoyin samar da makamashin da kuma hada miliyoyin ‘yan Nijeriya, wadanda har yanzu suke rayuwa cikin matsalar wutar lantarki, amma yanzu babban burinmu shi ne, samar da tsarin samar da wutar lantarki mai karfin mega wat 277, nan da shekarar 2060.

Cikar wannan buri, ya wuce batun zuba hannun jari kadai, domin yana bukatar kirkire-kirkire, bayar da gudunmawa a cikin gida da kuma sadaukarwa.

“Wannan shi ne dalilin da yasa taken taron na bana ya kasance a matsayin, Aiwatar da Manufofin Nijeriya na Farko da Gudanar da Ci gaban Abubuwan Cikin Gida da kuma Samar da Makamashi, yana da matukar muhimmanci. Kazalika, yunkurinmu na dabarun masana’antu a Nijeriya na kira gare mu da mu dage kan makomar hanyoyin samar da makamashi na Afirka a nan gida.”

Ya kara da cewa, a karkashin wannan, an hada sama da dala miliyan 400 na sabbin alkawuran saka hannun jari a bangaren sabunta makamashi mai a Nijeriya.

“Wannan ya hada da na’urorin hasken rana na sola da fanel-fanel, mita ta zamani, batiri da sauran makamantansu. Babu shakka, ana hasashen wadannan kayayyaki za su samar da ayyukan yi kai tsaye sama da 1,500 a fadin jihohi da dama da kuma nuna kwarin gwiwa a duniya, kan shirin samar da makamashi mai tsafta a Nijeriya”.

A nasa bangaren, Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ya ce; taron NRIP na 2025, ba wani taro ne da kawai aka shirya ba, sai dan shelanta cewa, Nijeriya a shirye take ta jagoranci sauye-sauyen makamashin da ake samu a Afirka.

Taken taron na bana shi ne, ‘Aiwatar da Manufofin Najeriya na Farko’, yana magana ne a kan wani abu mai mai muhimmanci da ya dara masana’antu, wanda ya kunshi jajircewa, kwarewar masana’antu da kuma dorewar tattalin arziki na tsawon lokaci.

“A bangaren samar da wutar lantarki, manufar Najeriya ta farko ta nuna aniyar tabbatar da cewa; zamani na gaba na fasahar samar da makamashi mai inganci, tun daga na’urori masu amfani da hasken rana har zuwa na’urorin adana makamashin batiri da aka baza a fadin kasar, na alfahari tare da dauke da lakabin, “Wanda aka samar a cikin gida Nijeriya’.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma October 17, 2025 Manyan Labarai Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura October 17, 2025 Labarai Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara October 16, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: samar da makamashi

এছাড়াও পড়ুন:

NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya

Hukumar Hana Safarar Mutane (NAPTIP) shiyyar Kano, ta kama wani mutum da ya yi yunƙurin safarar wasu mata bakwai zuwa Saudiyya.

Jami’an NAPTIP sun kai samame wani gida a Kano a ranar 2 ga watan Nuwamba, 2025, bayan samun bayanan sirri, inda aka ɓoye matan da ake shirin safararsu.

Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro

A cewar Mohammed Habib, Jami’in Hulɗa da Jama’a na NAPTIP a Kano, an ajiye matan a gidan ne yayin da ake shirin tura su Saudiyya domin yin aikatau.

Ya ce, “Bincike ya nuna cewa biyu daga cikin waɗanda aka ceto ’yan Nijar ne, yayin da biyar kuma ’yan Najeriya ne.”

Ya ƙara da cewa, “An kai matan Accra a Ghana, inda aka yi musu biza. Kuma duka aikin da za a musu bashi ne, inda kowacce za ta biya Naira miliyan 10, idan sun yi aikin wahala a Saudiyya .”

NAPTIP ta bayyana cewa an riga an kammala shirin tura matan filin jirgin saman Abuja a ranar 3 ga watan Disamba, 2025, wanda a nan aka shirya tafiyarsu Saudiyya.

Hukumar ta ce an kama mutum ɗaya, yayin da sauran waɗanda ke da hannu a lamarin suka tsere.

Jami’in, ya tabbatar da cewa hukumar na ci gaba da bincike domin kama sauran da suka tsere.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya