Cibiyar Tsare-tsaren Harkokin Ilimi da Gudanarwa ta Kasa (NIEPA) ta yaba da kokarin Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) wajen kare hakkokin yara na samun ilimi a Najeriya.

Darakta Janar na Cibiyar, Dakta David Shofoyeke ne ya bayyana hakan yayin bude taron horaswa na kwanaki uku ga masu gudanar da shirye-shiryen ilimin yankuna (LESOP) a Dutse, babban birnin Jihar Jigawa.

Dakta Shofoyeke, wanda Dakta Grace Omiyale Babbar Malamar Horaswa da Bincike a Cibiyar ta wakilta, ya tabbatar da cewa cibiyar tana da cikakken kudiri na sauya tsarin ilimi a Najeriya.

Ya bayyana cewa, samar da cikakken tsarin ilimi na jiha da kuma tsarin aiwatar da shirye-shiryen ilimi na jihohi yana taimakawa jihohi wajen tsara burinsu a fannin ilimi.

Ya ce, ta wannan hanya ce jihohi za su iya aiwatar da shirye-shiryen ilimi da suka dace da manufofi da albarkatun da ake da su.

Dakta David ya kara da cewa UNICEF tana bayar da taimakon fasaha wajen shirya wadannan takardu a jihohi takwas.

A cewar NIEPA, UNICEF ta shimfida tubalin shirye-shiryen ilimi bisa hujja, masu daidaito tsakanin jinsi, da fama da nakasassu, tare da karfin jurewa rikice-rikice da sauyin yanayi a Najeriya.

Dakta David ya yaba wa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa jajircewarta wajen sauya tsarin ilimi ta hanyar amfani da bayanai wajen yanke shawara.

 

Shi ma babban  sakatare na ma’aikatar ilimin gaba da sakandare, da fasaha da kimiyya ta jihar, Alhaji Muhammad Dahiru, ya yaba wa abokan hulɗa bisa shawarwarin  da suke bayarwa.

A cewarsa, Gwamnatin Jihar Jigawa tana da cikakken kudiri na yin aiki tare da abokan hulda domin samar da ingancin ilimi a jihar.

Dahiru ya ce daya daga cikin ginshikan gwamnatin Namadi shi ne sauya tsarin ilimi.

Hukumar UNICEF tare da hadin gwiwar Tarayyar Turai (EU), suna tallafa wa Jihar Jigawa wajen nazarin sabon tsarin dabarun ilimin jihar.

Wannan aikin yana gudana ne karkashin shirin hadin gwiwa na UNICEF da EU kan ilimi da karfafa matasa.

 

Usman Mohammed Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa shirye shiryen ilimi Jihar Jigawa tsarin ilimi

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Cutar kansar mama na ɗaya daga cikin manyan cututtukan da ke addabar mata a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

 

An kiyasta cewa mata sama da dubu ɗari biyu na kamuwa da cutar a kowace shekara a Najeriya, yayin da miliyoyin mata a duniya ke fama da wannan cuta. Abin damuwa shi ne cewa yawancin lokuta ana gano cutar ne a kurarren lokaci, wanda hakan ke sa magani ya yi wahala kuma ya rage yiwuwar ceto rayuwar wanda ya kamu da shi.

NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa
  • Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro  
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo