Aminiya:
2025-12-02@20:45:29 GMT

Ta’addanci: An fi kashe Musulmi a kan Kiristoci a Najeriya — Jakadan Amurka

Published: 18th, October 2025 GMT

Jakadan Amurka na Musamman kan Harkokin Larabawa da Afirka, Massad Boulos, ya ƙaryata iƙirarin cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya babu gaira babu dalili.

Ya ce hare-haren ta’addanci da ke faruwa a ƙasar suna shafar Kiristoci da Musulmai baki ɗaya.

An rantsar da Randrianirina shugaban Madagascar Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata

Boulos, wanda mashawarci ne ga Shugaban Amurka Donald Trump, ya faɗi hakan ne bayan ganawarsa da Shugaba Bola Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, a ranar Jumma’a.

Wasu ’yan majalisar dokokin Amurka sun nemi gwamnatin Amurka ta sanya Najeriya cikin jerin ƙasashe masu hatsari wadda ake zaluntar Kiristoci.

Sai dai Jakadan ya ce lamarin ba haka yake ba.

“Waɗanda suka san Najeriya sosai sun fahimci cewa ta’addanci ba shi da launi, addini, ko ƙabila,” in ji Boulos.

“Kungiyoyin Boko Haram da ISIS sun kashe Musulmai sama da Kiristoci. Mutane daga kowane ɓangare na fama da wannan tashin hankali. Ba a iya wani ake kai wa hari ba.”

Ya bayyana cewa rikicin da ake samu a Arewa ta Tsakiya a Najeriya, rikici ne tsakanin manoma da makiyaya, wani lokaci yana shafar Kiristoci, amma asalin rikicin yana da nasaba da harkar noma, ba addini ba.

“Ba shi da nasaba da addini,” in ji shi.

“Najeriya ƙasa ce da ta ƙunshi ƙabilu da addinai da dama waɗanda suke zaune tare tsawon shekaru. Bai kamata a juya wannan matsala zuwa ta koma ta addini ba.”

Boulos, ya kuma yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu bisa ƙoƙarin da ta ke yi wajen inganta tsaro, inda ya ce sakamakon ƙoƙarin ya fara bayyana.

Maganar “kisan gillar Kiristoci” a Najeriya ta ƙara yawaita ne bayan jawabin Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima a taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA).

A yayin taron ya yi kira da a samar da zaman lafiya a Gaza da kuma goyon bayan tsarin ƙasashe biyu tsakanin Isra’ila da Falasɗinu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: rikicin manoma da makiyaya taro tattaunawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta

Hukumomi a Gaza sun ce akalla Falasdinawa 357 ne sukayi shahada yayin da wasu 903 suka jikkata a hare-haren Isra’ila tun bayan da yarjejeniyar tsagaita wuta ta fara aiki a ranar 10 ga Oktoba.

Yawancin wadanda abin ya shafa mata ne da yara, in ji ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza a cikin wata sanarwa.

A cewar ofishin, sojojin Isra’ila na kuma tsare da mutane 38 ba bisa ka’ida ba.  

ofishin ya ce ya lissafa laifukan tsagaita wuta guda 591, ciki har da harbi kai tsaye kan fararen hula, gidajensu, da tantuna, da kuma bama-bamai da rushe gidaje.

Sanarwar ta ce, wadannan laifukan, suna “nufin mamayar na wargaza yarjejeniyar da kuma haifar da mummunan yanayi wanda ke barazana ga tsaro da kwanciyar hankali a yankin Gaza.”

Ofishin ya yi kira ga Shugaban Amurka Donald Trump, da masu shiga tsakani da kuma masu ba da garantin tsagaita wutar, da kuma Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da su dauki matakai masu inganci don kawo karshen hare-haren Isra’ila da kuma tilasta wa Tel Aviv ta bi dukkan ka’idojin yarjejeniyar.

Yarjejeniyar tsagaita wuta, wacce Turkiyya, Masar, da Qatar suka shiga tsakani tare da goyon bayan Amurka, ta fara aiki a ranar 10 ga Oktoba don kawo karshen hare-haren Isra’ila na shekaru biyu da suka kashe mutane sama da 70,000, galibi mata da yara, tare da jikkata sama da 170,000 tun daga watan Oktoban 2023.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Tawagar ECOWAS za ta je Guinea-Bissau, bayan juyin mulkin soji December 1, 2025 Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran December 1, 2025 Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi December 1, 2025 Maduro Ya Gargadi Amurka Game Da Hankoron Mamaye Rijiyoyin Mai Na Venezuela December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban  “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufar
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta
  • Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi
  • Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki