Georgieba ta kuma gargadi duniya kan barazanar da fitar da kudade ta haramtacciyar hanya (IFFs) ke yi, inda ta ce wannan matsala ta zama babbar abin da ke lalata tattalin arziki da tsarin kudi na kasashe a fadin duniya.

 

A cewarta, fitar da kudade ta haramtacciyar hanya wacce ta hada da satar kudaden gwamnati, kudaden da suka fito daga ayyukan laifi, da mu’amalolin dijital da ba a iya bibiyarsu na ci gaba da lalata tsarin mulki, rage kudaden gwamnati, da durkusar da kokarin ci gaba, musamman a kasashe masu tasowa.

 

A cikin wani jawabin manufofi na baya-bayan nan, jami’an IMF sun bayyana cewa IFFs yanzu suna zuwa ta fannoni da dama. Wannan ya hada da karkatar da kudaden haraji kai tsaye zuwa aljihun wasu mutane da kuma karkatar da kudaden masu zaman kansu zuwa haramtattun harkoki da ke barazana ga jin dadin kasa.

 

Sun kara da cewa tattalin arzikin dijital ya kara tsananta wannan matsala, inda kudaden dijital kamar Bitcoin ke ba da damar yin mu’amalolin kudi ba tare da a san masu aikata su ba.

 

Shugabar IMF ta ce: “Za ka iya samun kudi, kudin da aka sace kai tsaye daga al’ummar masu biyan haraji. Haka kuma akwai kudaden masu zaman kansu da ake karkatawa zuwa ayyukan laifi da ke lalata jin dadin ‘yan kasa.”

“Yanzu da kudaden dijital, ana iya tallafa wa ayyukan laifi ba tare da a gano su ba. Wannan babbar matsala ce, kuma dole ne mu dauke ta da muhimmanci.”

Dabarar IMF Wajen Yakar Kudaden Haram:

A martaninta, IMF ta bayyana cewa ta karfafa tsarinta na yaki da safarar kudade da kuma hana tallafa wa ta’addanci (AML/CFT) bayan cikakkiyar bita da aka gudanar a shekarar 2023.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili October 18, 2025 Labarai Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu October 17, 2025 Labarai Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja October 17, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama ’yan bindiga 4 a Kano

An kama wasu mutum huɗu da ake zargin ’yan bindiga ne ɗauke da makamai da ake zaton bindigogi ne a tashar mota ta Ƙofar Ruwa da ke Jihar Kano.

Tashar motar, wadda ke kusa da kasuwar kayan gini ta Ƙofar Ruwa a Ƙaramar Hukumar Dala.

MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a

A cewar mazauna yankin, an kama mutanen ne lokacin da suke ƙoƙarin shiga mota domin tafiya zuwa wani waje a cikin Kano.

“Mutanen da ke tashar motar ne suka lura da makaman da suke ɗauke da su. Take suka gaggauta sanar da jami’an tsaro, waɗanda suka kama su. Su huɗu ne gaba ɗaya,” in ji Musa Balarabe, wani mazaunin yankin.

Ya ce an kama su ne da misalin ƙarfe 1 na rana.

Da farko an kai su ofishin ’yan sanda na Ƙofar Ruwa, kafin daga bisani aka mayar da su ofishin Dala.

Wani mazaunin yankin, Umar Nuhu, ya ce yana cikin shagonsa da ke Kwanar Taya, kusa da ofishin ’yan sandan, lokacin da aka kawo mutanen.

Ya ce hakan ya jawo firgici, inda mutane suka fara gudu a ko’ina.

Nuhu, ya ƙara da cewa mutane da yawa sun yi dandazo a ofishin ’yan sandan, yayin da wasu matasan ke son ɗaukar doka a hannu.

Da aka tuntuɓi kakakin ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, bai ce komai kan lamarin ba.

Ya ce har yanzu suna tattara bayanai kafin su fitar da sanarwa.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sabuwar sanarwa daga rundunar ’yan sandan jihar.

Tashar Kofar Ruwa, tasha ce da ke jigilar fasinjoji zuwa jihohi irin su Katsina, Jigawa, Sakkwato, Zamfara, Kebbi, har ma da Jamhuriyar Nijar.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Jihar Kano ke fama da hare-haren ’yan bindiga, musamman a yankunan da ke da iyaka da Jihar Katsina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku