Arsenal Na Dab Da Daukar Dan Wasan Gaba Viktor Gyokeres
Published: 21st, May 2025 GMT
Kungiyar Arsenal na shirin ɗaukar ɗan wasan gaban Sporting CP, Viktor Gyokeres kamar yadda jaridar wasanni ta football365 ta ruwaito.
Arsenal ta fuskanci matsalolin ‘ƴan wasan gaba a kakar wasan da ke dab da ƙarewa, yayin da ƙungiyar ta gaza lashe kowane irin kofi.
Bayan ƙarewa a mataki na biyu a Gasar Premier da samun gurbin zuwa Gasar Zakarun Turai ta baɗi, a yanzu hankalin ƙungiyar ya karkata kan samun ɗan wasan gaba, domin sake gina kanta.
A ƙarshen kakar wasa da muke ciki ne Gyokeres ɗan asalin Sweden zai bar ƙungiyar Sporting bayan ƙarewar kwantiraginsa, kamar yadda Fabrizio Romano fitaccen ɗan jaridar wasanni ya bayyana a shafinsa na X.
BBC
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Maduro Ya Jinjina Wa Jagororin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
Shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro wanda ya bude bikin baje kolin littatafai na kasa da kasa a kasarsa, ya yi jinjina ga Imam Khumaini ( r.a) da kuma jagoran juyi Ayatullah Sayyid Ali Khamnei.
Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto cewa, A yayin bikin bude taron baje kolin, shugaban kasar na Venezuela ya bayyana girmamawar da yake yi wa jagoran juyin musulunci, tare da yin ishara da ganawarsu a shekarun 2000 da 2010.
Haka nan kuma shugaban kasar ta venezuella ya bayyana yadda ya ga al’adu da ci gaban al’ummar Iran da su ka ja hankalinsa da burge shi matuka.
Bugu da kari shugaba Maduro ya bayyana zurfin hikimar da ya gani a tare da jagoran juyin musulunci, da kuma yadda yake kare tsarin jamhuriyar musulunci da ci gaba da wanzuwarsa a cikin nutsuwa, hakuri, juriya da kuma tsayin daka.
Har ila yau, shugaba Maduro ya yi ishara da yadda Iran take cika alkawalinta a fagen kawancenta da kasarsa Venezuela.