Babban Mufti na kasar Oman ya bayyana cewa: Matakin taron kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ya fi kankara sanyi da rashin muhimmanci

Babban Mufti na masarautar Oman, Sheikh Ahmed bin Hamad Al-Khalili, ya jaddada yabonsa ga fitaccen matsayi na kasar Yemen da kuma matsin lamba da dakarun kasar Yemen suke yi na kai kayan agaji a zirin Gaza.

A gefe guda kuma, ya nuna rashin jin dadinsa da raunin kudirin taron kasashen Larabawa kan daukan matakan matsin lamba kan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da take aiwatar da kashe-kashen gilla kan al’ummar Falasdinu.

A wani rubutu da ya yi a dandalin X, Al-Khalili ya bayyana godiyarsa ga jaruman kasar Yemen da kuma kasashen da suka bayar da gudumawa wajen matsin lamba don saukaka shigar da kayan agaji Gaza, yana mai cewa, “Ya gode wa Allah da shigar da wasu agajin da aka yi a Gaza,” yana mai jaddada bukatar ci gaba da daukan matakan matsin lamba na kasa da kasa wajen bude mashigar agaji gaba daya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Amurka Ya Zanta Ta Wayar tarho Da Benyamin Natanyahu Dangane Da Iran Da Gaza

Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya zanta ta wayar tarho da firay ministan HKI Benyamin Natanyahu kan kasar Iran da kuma yakin Gaza.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa majiyar ofishin Natanyahu ta bayyana cewa tattaunawar tana zuwa ne a dai-dai lokacinda rikici da yaki yake ci gaba a gaza, da kuma tattaunawa kan shirin Nuclear kasar Iran ke ci gaba.

Labarin ya kara da cewa shugaban kasar Amurka na jirin jawabin da kasar Iran zata mayar masa dangane da shawarar da ya gabatar na warware matsalar tashe makamancin Yuranium a Iran.

Har’ila yau ya na jiran jawabin da kungiyar Hamas za ta bayar kan yarjeniyar  dakatar da yaki a Gaza.

Shugaban dai yana cikin matsin lamba don ganin an warware wadannan al-amura guda biyu na gabas ta tsakiya.

Tattaunawar wanda bai fi mintoci 40 ba, ya bukaci gwamnatin Natanyaho ta shirya daukar matakan gaggawa bayan da shugaban ya sami wadannan sakonnin da yake jira.

Don haka ne ake saran Natanyanhu zai gudanar da taron gaggawa tare da manya manyan jami’an gwamnatinsa a ma’aikatar tsaro ko yakin na kasar, don tattauna wadannan al-amura.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
  • Shugabannin Sin Da Kongo (Brazaville) Sun Aike Da Wasikun Taya Murna Ga Taron Ministocin Kula Da Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC
  • Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji
  • Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu
  • Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna
  • Za’ayi tattaunawa ta gaba tsakanin Iran da Amurka a ranar Lahadi a Oman
  • Jami’in Makamashin Nukiyar Iran Ya Ce; Zarge-Zargen Da Ake Yi Kan Shirin Makmashin Nukiliyar Iran Siyasa Ce Kawai
  • Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Babban Darektan Hukumar IAEA Saboda Yadda Yake Mika Wuya Ga Bakar Siyasa
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Zanta Ta Wayar tarho Da Benyamin Natanyahu Dangane Da Iran Da Gaza