Shugaban kasar Angolan João Lourenço, wanda kuma shi ne ke rike da shugabancin karba-karba na kungiyar tarayyar Afirka (AU) ya yi kira ga gwamnatin Congo Democradiyya da mayakn M-23 su kawo karshen yaki kafin taron tattauna batun tsagaita wuta a gabacin kongo nan gaba.

Shafin yanar gizo na labarai ‘Afirca News” ya nakalto shugaban yana kira ga bangarorin biyu su tsagaita wuta da misalign tsakiyar daren jiya Lahadi don a tattauna batun samar da zaman lafiya cikin Nutsuwa.

Majiyar fadar shugaba Lourenco na cewa yakamata tsagaita wutan ya hada har da rashin kokarin mamayar karin iko a wasu wurare. Da kuma dakatar da fada. Da kashe fararen hula da sauransu.

An shiya cewa gwamnatin kongo Democradiyya da kuma wakilan yan tawayen M-23 zasu hadu a karon Farko don tattauna batun tsagaita budewa Juna wuta da kuma kawo karshen yakin a ranar 18 ga watan Maris, wato gobe talata , a birnin Luanda babban birnin kasar ta Angola.

Gwamnatin Kongo Democradiyya dai bata bayya a fili zata halarci taron sulhun wanda kasar Angola ta shirya ba, amma M-23 ta nuna goyon bayanta ga shirin na kasar Angola. Sai dai ta yikira ga shugaba Tsetsekedi ya bayyana anniyarsa ta zuwa taron sulhun a fili.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata

Shugaban kasar Siriya ya ki amincewa da bukatar kurdawan kasar daga dakarun Democradiyyan  kurdawa wato (SDF), na samar da tsarin tarayya a kasar bayan kifar da gwanatin Basshar Al-Asab.

Jaridar The Nation ta nakalto shuga Al-Ahmad Sharaa yana fadar haka a jiya Lahadi ya kuma kara da cewa tsarin tarayyar barazana ce ga hadin kan kasar ta Siriya sannan tsarin tarayya ya sabawa yarjeniyar da aka kulla da kurdawan a baya-bayan nan.

A wani taron da suka gabatar a makon da ya gabata,  jam’iyyar kurdawan kasar ta Siriya (SDC) ta fadawa “ The National  ”  bayan taron kan cewa suna bukatar tsarin tarayyar a kasar Siriya don shi ne kadai zai tabbatar da hakkinsu a kasar.

A cikin watan maris da ya gabata ne shugaba Al-Sharaa na kasar Syriya ya rattaba hannu a kan wata yarjeniya da shugaban dakarun kurdawan kasar Siriya SDF Mazlum Abdi dangane da hade dakarunsa da sojojin kasar Siriya, sannan yace tsarin tarayya ya sabawa wannan yarjeniyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar