Malaman Makarantun Firamare 1,800 Sun Samu Horo Aka A Kwara
Published: 10th, April 2025 GMT
Akalla malaman makarantun firamare 1,800, a fadin kananan hukumomi goma sha shida na jihar Kwara, aaka horar da su kan kara kuzari kan ilimin zamani, hanyoyin amfani da kayan zamani wajen koyarwa.
Da yake bayyana taron bitar na kwanaki goma da aka bude a makarantar sakandire ta Queen Elizabeth da ke Ilorin wanda KwaraLEARN tare da hadin gwiwar hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar Kwara (KWSUBEB) ta shirya, kwamishinan ilimi da ci gaban bil’adama na jihar, Dokta Lawal Olohungbebe ya ce shirin na daya daga cikin manyan dabarun da jihar ta bullo da shi na bunkasa harkar ilimi domin ya dace da ka’idojin karni na 21.
Ya kuma bukaci malaman da su ci gaba da jajircewa wajen tsara makomar jihar ta hanyar baiwa al’umma da ilimi da kyawawan dabi’u.
Dokta Olohungbebe ya jaddada shirye-shiryen jihar na tallafa wa ingancin malamai ta hanyar ci gaba da horar da su tare da kayan aikin zamani, a matsayin wani bangare na tafiyar da gwamnati daga tsohon tsari zuwa tsarin ilimin dijital ko zamani.
Kwamishinan ya bayyana kwarin gwiwar cewa horon zai yi tasiri sosai a cikin aji.
Ya bukaci mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da suka samu domin ci gaban dalibansu da kuma bangaren ilimi gaba daya.
A nasa jawabin Manajan Darakta na KwaraLEARN, Misis Laide Abel, ta taya mahalarta taron murnar samun horon.
Ta kwadaitar da su da su mai da hankali da kuma taka rawar gani a duk tsawon zaman domin samun cikakkiyar fa’ida daga shirin.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Gwamnatin tarayya ta ɗauki nauyin dukkanin buƙatun ɗaliban na zana jarabawar, ciki har da abinci da wurin kwana, har na tsawon kwanaki uku. Kwamishinan ilimi na jihar Bauchi, Dakta Lawal Mohammed Rimin Zayam, ya yaba da wannan mataki na JAMB, yana mai kira ga iyaye da su tura ‘ya’yansu dake da lalura ta musamman makaranta domin samun ilimi.
Kwamishinan ya kuma yi kira ga al’umma da iyaye su fahimci muhimmancin ilimi, musamman ga yara masu naƙasa, yana mai cewa gwamnati za ta ci gaba da wayar da kan iyaye don ganin suna tura ‘ya’yansu makaranta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp