Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
Published: 15th, June 2025 GMT
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun yi bayani kan sabon salon mayar da martani kan Isra’ila a harin ‘Alkawarin Gaskiya na 3″
Ma’aikatar hulda da jama’a ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran a cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin jiya Asabar ta sanar da cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC sun kaddamar da wani sabon farmakin hadin gwiwa na “Alkawarin Gaskiya na 3” ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jirage masu saukar ungulu a matsayin mayar da martani ga sabon farmakin da yahudawan sahayoniyya suka yi kan yankunan Iran.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar hulda da jama’a ta IRGC ta fitar ta bayyana cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC sun kaddamar da wani sabon salon farmakin hadin gwiwa na “Alkawarin Gaskiya na 3” kan yankunan haramtaciyar kasar Isra’ila da muhimman cibiyoyinta ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jirage marasa matuka don mayar da martani ga sabon harin wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suka yi kan yankunan kasar Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun sanar a cikin wani sako mai cike da alhini da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun IRGC wanda ya yi shahada da asubahin ranar Juma’ar nan yayin wani hari na ta’addanci” da gwamnatin sahyoniyawan ta kai kan hedkwatar rundunar.
Hukumar soji tana jinjinawa wannan babban kwamandan da aka gabatar a matsayin babban jigo wajen kare manufofin juyin juya halin Musulunci na Iran, tare da yin alkawarin mayar da martani mai tsauri ga makiya.
Ga yadda sanarwar IRGC ta kasance :
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
A cikin bakin ciki da radadi muna sanar da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci, da da wasu mukarabansa, a lokacin harin ta’addancin da gwamnatin sahayoniya ta kai a safiyar wannan ranar ta Juma’a akan hedkwatar IRGC yayin da suke gudanar da muhimmin aiki na tsaron kasa.
Muna mika ta’aziyyarmu ga Jagoran juyin juya halin Musulunci kuma babban kwamandan sojojin kasar, Imam Khamenei, da iyalan duk wadanda abun ya shafa.
Duk da wannan harin na dabbanci, muna tabbatar wa al’ummar Iran masu daraja cewa, har yanzu rundunar sojojin Iran a shirye suke don maida martani ga gwamnatin sahyoniyawan.
Nan ba da jimawa ba za a isar da cikakken bayani kan halin da ake ciki biyo bayan harin na makiya da kuma matakin da za a dauka na hukunta su.
Haka zalika kafofin yada labarai na Iran sun rawaito shahadar babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Mohammad Hossein Baqeri.
Shi ma Manjo Janar Baqeri ya yi shahada a wani harin ta’addanci da gwamnatin sahyoniya ta kai birnin Tehran a safiyar yau Juma’a.