HausaTv:
2025-06-01@23:21:37 GMT

Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka

Published: 1st, March 2025 GMT

Fira ministan hakar Habasha  Abiy Ahmed ya sami kyakkyawar tarba daga shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mamhud a birnin Mogadishu na Habasa a ranar Alhamis da ya kai ziyara domin bunkasa alaka a tsakainin kasashen biyu.

Sabani a tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna ya kunno kai ne a shekarar da ta gabata, bayan da kasar ta Habasha ya kulla yarjejeniya da yankin Somaliland akan tashar jirgin ruwa.

Ita dai kasar ta Habasha ba ta da iyaka da ruwa, don haka take son amfani da mashigar ruwan kasar ta yankin Somaliland. Habashan dai tana son gina wani yanki na kasuwanci a gabar ruwan  ta yankin Somaliland.

 Yankin Somaliland na kasar Somaliya ne wanda Mogadishu  take daukar cewa ba kasa ce mai cin gashin kanta.

Somaliya ta nuna fushinta akan waccan yarjejeniyar tare da zargin Habasha da yin kuste a cikin iyakokin kasarta.

A cikin watan Disamba ne dai Turkiya ta fara shiga tsakanin kasashen biyu domin  warware sabanin da yake a tsakaninsu.

Tattaunawar ranar Alhamis din a tsakanin kasashen biyu ta mayar da hankali ne akan kasuwanci, da tsaro da kuma batun sake mayar da alakar da diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Makaman nukiliya ba su da gurbi a cikin akidar Jamhuriyar Musulunci ta Iran

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Iran ba za ta taba yin watsi da haƙƙin da doka ta tanada ba ta fannin inganta sinadarin uranium, domin inganta harkar kiwon lafiya, aikin gona da masana’antu, yana mai jaddada cewa: makaman nukiliya ba su da gurbi a cikin koyarwar Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

A yayin ziyarar da ya kai masarautar Oman, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, a wata hira da gidan talabijin na kasar, ya yi bayani kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu, da kuma muradun yankin da na kasa da kasa na Iran da Oman, da kuma muhimman batutuwan da suke faruwa a duniya.

Ya kamata a lura da cewa: Wannan ziyara ta zo ne a cikin tsarin karfafa zumunci da fitacciyar alakar da ke tsakanin masarautar Oman da Jamhuriyar Musulunci ta Iran, da goyon bayan bangarori daban-daban na hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, da kuma cikin tsarin muradun da shugabannin kasashen biyu ke da shi na kara karfafa da raya wannan dangantaka. An tattauna fannoni daban-daban na hadin gwiwa da suka yi daidai da muradun kasashen abokan juna da kuma biyan bukatunsu, musamman ma a fannin ci gaban yankin da kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Yankunan Kasar Siriya Tare Da Kafa Wuraren Bincike
  • Oman ta mika wa Iran takardun shawararin Amurka game da tattaunawar nukiliya
  • Isra’ila ta hana tawagar kasashen Larabawa shiga gabar yammacin kogin Jordan
  • Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
  • Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”
  • Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran