An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
Published: 1st, March 2025 GMT
Cecekucen dai a tsakanin Donald Trump da kuma Vladmir Zylinesky an yi shi ne saboda banbancin ra’ayin da bangarorin biyu suke da shi akan batun kawo karshen yakin Ukiraniya.
Shugaban Amurka Donald Trump dai yana son ganon takwaransa na Ukiraniyan ya amince da kawo karshen yankin da kasarsa take yi da Rasha, yayin da Zylinesky yake Magana akan wasu sharudda kafin hakan ta faru.
Shugaban kasar Amurkan ya yi wa shugaban kasar Ukiraniya goron cewa, kasarsa ce take ba su taimakon kudade da makamai, yana mai kara da cewa; Ko dai ya amince da kulla yarjejeniyar kawo karshen yakin ko kuma Amurka ta dakatar da duk wani taimako.
Haka nan kuma shugaban na Amurka ya zargi shugaban Ukiraniya da cewa, yana son kunna wutar yakin duniya na uku,alhali bai taki komai ba.
Shi kuwa mataimakin shugaban kasar Amurka ya zargi Zylenisky da cewa , babu girmamawa ga Amurka da shugaban kasarta a cikin abinda yake yi..”
Shi kuwa shugaban kasar ta Ukiraniya ya ce, babu yadda za ayi , ya yi sasauci a gaban Putin na Rasha.”
Shugaban na Ukiraniya ya fice daga fadar White House ba tare da gabatar da taron manema labaru ba, kamar yadda tun da fari a ka tsara za a yi.
Bayan tafiyar tashi ne dai shugaban Amurka ya wallafa sako a shafinsa na “Truth Social” da a ciki ya bayyana cewa: Zylinesky ya wulakanta Amurka, amma zai iya dawowa idan ya shirya karbar zaman lafiya.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
Fadar Shugaban ƙasa ta bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarin wa’adin shekara guda ga shugaban hukumar Kwastan ta Nijeriya, Bashir Adewale Adeniyi.
Kafin wannan ƙarin wa’adin, aikin Adeniyi zai kare ne a ranar 31 ga Agusta, 2025. Sai dai sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis ta ce wannan mataki na Tinubu zai ba Adeniyi damar kammala muhimman gyare-gyare da ayyuka da gwamnatin ke aiwatarwa a hukumar.
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da GidajeA cikin manyan ayyukan da ake son a kammala akwai shigar da cigaban zamani da ake yi wa hukumar Kwastan, da aiwatar da tsarin “National Single Window Project” da kuma cika alƙawuran Nijeriya a ƙarƙashin yarjejeniyar cinikayyar Afrika (AfCFTA).
“Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya” in ji sanarwar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp