Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-07@13:17:16 GMT

Gwamnan Zamfara Ya Yi Jajen Rasuwar Dan Majalisa Aminu K/Daji

Published: 10th, April 2025 GMT

Gwamnan Zamfara Ya Yi Jajen Rasuwar Dan Majalisa Aminu K/Daji

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya nuna kaɗuwar sa bisa rashin da aka yi na ɗan Majalisar Dokokin jihar, Hon. Aminu Ibrahim Kasuwar Daji, ɗan Majalisa mai wakiltar mazaɓar Ƙauran Namoda ta Kudu.

Iyalai sun bayyana cewa Hon. Aminu Kasuwar Daji ya rasu ne a cikin barcin sa da asubahin ranar Larabar nan a Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa gwamnan ya miƙa ta’aziyyar sa ga Majalisar Dokokin jihar da Iyalan mamacin.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnatin jihar ta aika da tawaga ta musamman, ƙarƙashin jagorancin mataimakin gwamnan jihar, Mallam Mani Mummuni a yayin jana’izar ta marigayi Aminu K/Daji in Kauran Namoda.

“A madadin gwamnatin jiha,muna miƙa saƙon ta’aziyyar mu ga shugaban Majalisar Dokokin, sauran shugabanni a Majalisar, iyalai da al’ummar Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda ta Kudu.

“Muna kuma yin addu’a Allah ƙara ma iyalai jimirin jure wannan rashi. Muna kuma addu’ar Allah gafarta wa marigayin kurakuran sa.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rasuwa Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da kyautar fuloti da kuɗi naira miliyan biyar ga kowane ɗaya daga cikin iyalan tawagar ’yan wasan nan na Kano 22 da suka rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya auku a watan Yuni.

Mai bai wa gwamnan shawara kan yaɗa labarai, Ibrahim Adam, ne ya tabbatar da wannan kyauta cikin wani saƙo da ya wallafa a Facebook a wannan Larabar.

Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina

“Mai girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bai wa iyalan ’yan wasan da suka rasu fuloti ɗaya da kuma naira miliyan biyar kowannensu,” in ji sanarwar.

Aminiya ta ruwaito cewa, tawagar ’yan wasan da suka rasu ta yi hatsari ne a yayin da suke dawowa daga gasar wasannin ƙasa ta National Sports Festival da aka gudanar a Jihar Ogun.

Tawagar da lamarin ya rutsa da ita ta ƙunshi ’yan wasa, masu horarwa, mataimakansu, jami’an lafiya, direbobi, injiniyoyi da kuma ɗan jarida.

Ajali ya katse musu hanzari ne bayan samun nasarori daban-daban a gasar ta National Sports Festival da suka haɗa da sarƙoƙin zinare 6, azurfa 13 da na tagulla 10 da suka lashe.

Ana iya tuna cewa, mummunan lamarin ya auku ne a garin Dakatsalle da ke ƙaramar hukumar Bebeji, kimanin kilomita 50 daga Kano, a yayin da ya rage ƙiris tawagar ta ƙarasa gida.

Tun a wancan lokaci, jama’a daga ciki da wajen Jihar Kano suka riƙa jimami da bayyana alhini, musamman duba da irin gudummawar da ’yan wasan suka bayar kafin rasuwarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Taraba
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Tataba
  • Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi
  • Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki
  • Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina
  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
  • Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
  • Mu daina zagin malaman addini idan muna son zaman lafiya — Uba Sani
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara