Aminiya:
2025-09-17@23:19:48 GMT

Ƙasashen AES sun kafa gidan rediyo don yaƙar farfagandar turawa

Published: 24th, April 2025 GMT

Ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso, ƙarƙashin inuwar Ƙungiyar Ƙasashen Sahel (AES), sun sanar da shirinsu na ƙaddamar da gidan rediyo na haɗin gwiwa.

Ƙasashen guda uku, waɗanda duk a halin yanzu suke ƙarƙashin mulkin soja, sun jaddada cewa sun kafa gidan rediyon ne da nufin daƙile farfagandar ƙasashen waje da kuma isar da “ingantattun bayanai na gaskiya” ga ’yan ƙasarsu.

Sanarwar tasu ta kasance bayan ƙaddamar da gidan talabijin ɗinsu na intanet na haɗin gwiwa da suka yi a watan Disamba na 2024, wanda suka bayyana a matsayin dandamali da aka samar domin “yaƙi da yaɗa labaran ƙarya.”

Baya ga waɗannan ayyukan watsa labarai, a baya ƙungiyar ta nuna sha’awarta ta kafa kamfanin jiragen sama na yankin da kuma bankin saka hannun jari, wanda ya ƙara nuna jajircewarsu ga haɓaka haɗin kai da ci-gaba a tsakanin ƙasashe mambobin AES.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya

A watan Janairu na 2025 ne  ƙasashen uku da suka kafa ƙungiyar ta AES, suka sanar da ficewarsu a hukumance daga Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS).

Makonni uku da suka gabata, ƙasashen da ke ƙarƙashin mulkin sojoji, sun ɗora harajin shigo da kaya na kashi 0.5 bisa ɗari a kan kayayyaki daga ƙasashen ECOWAS.

Harajin ya shafi duk kayayyakin da suka shigo daga ƙasashen ECOWAS zuwa kowace daga cikin ƙasashen uku, banda kayan agajin jin kai.

Wannan tsarin ya yi karo da shirin ECOWAS na tabbatar da zirga-zirgar kayayyaki a tsakanin mambobinta da ƙasashen AES duk da ficewarsu a hukumance daga ƙungiyar a watan Janairu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ECOWAS haɗin gwiwa Nijar

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff