Aminiya:
2025-07-06@16:25:37 GMT

Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC

Published: 6th, July 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ƙaryata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa zai bar jam’iyyar APC zuwa ADC tare da wasu gwamnoni biyar.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Dauda Iliya, ya fitar, Zulum ya ce wannan labari ƙarya ne, kuma wasu ne kawai ke ƙirƙirarsa domin cimma wata manufa ta ƙashin kansu.

Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha

Ya ce yana nan daram a jam’iyyar APC kuma yana biyayya ga jam’iyyar a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya.

Sanarwar ta ce, “Mun ji wani labari da ake yaɗawa cewa zan koma jam’iyyar ADC tare da wasu gwamnoni biyar.

“Wannan labari ba gaskiya ba ne. Waɗanda suka ƙirƙira shi ba sa kishin ƙasa kuma ba sa taimaka wa Jihar Borno ko Nijeriya.”

Zulum ya ƙara da cewa yana nan daram a APC, domin ya damu da ci gaban Jihar Borno.

“Ina roƙon jama’ar Borno da su yi watsi da wannan jita-jita. Mu ba mu da lokacin siyasar da ba ta da amfani. Muna da aiki a gabanmu na ci gaban jiharmu,” in ji shi.

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su tabbatar da sahihancin labarai kafin su yaɗa su.

Hakazalika, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki tuƙuru a ƙarƙashin jam’iyyar APC domin ciyar da jihar gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPP

Jam’iyyar NNPP, ta bayyana cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yi mata takarar shugaban ƙasa a 2023, ba zai tsaya takara a 2027 ba.

Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dokta Agbo Major, ne ya bayyana haka a wata sanarwa, inda ya mayar da martani kan wata magana da Buba Galadima ya yi.

Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung Tsadar rayuwa ta sa ’yan Nijeriya na siyan abincin da ya lalace

Galadima, ya ce har yanzu Kwankwaso yana cikin NNPP kuma zai tsaya takara a 2027.

Galadima ya shaida wa manema labarai cewa: “Babu wani tabbaci da ke nuna cewa Kwankwaso yana shirin komawa APC. Za mu ci gaba da zama a NNPP har lokacin zaɓen 2027 ya zo. Muna kira ga ’yan Najeriya su mara masa baya.”

Amma shugaban NNPP ya musanta hakan, inda ya ce: “Kwankwaso da Galadima tun tuni aka kore su daga jam’iyyar. Ba su da hurumin magana a madadin NNPP ko amfani da ita domin yin takara,” in ji Major.

Ya bayyana cewa tafiyar NNPP da Kwankwasiyya ta ƙare tun bayan zaben shugaban ƙasa na 2023.

“Yarjejeniyarmu da Kwankwasiyya ta ƙare bayan zaɓen 2023. Ba za mu amince Kwankwaso ya dawo ba saboda matsalolin da ya janyo mana ba,” in ji shi.

Dokta Major, ya kuma zargi Kwankwaso da yunƙurin karɓe ragamar jam’iyyar ta ƙarfi da yaji.

“Kwankwaso ya canja tambarin jam’iyya zuwa na Kwankwasiyya ba tare da izini ba, kuma ya jefa mu cikin rikicin shari’u marasa tushe. Sai da aka kai kotu kafin INEC ta dawo da tambarinmu na asali,” in ji shi.

Ya ce Kwankwaso yana fatan sake samun damar tsayawa takara kamar yadda ya yi a 2023, amma hakan ba yiwuwa ba.

“Yana tsammanin zai sake samun tikitin takara kamar yadda ya samu a baya, amma hakan ba zai faru ba,” a cewarsa.

Ya ƙara da cewa: “An kori Kwankwaso da tawagarsa daga jam’iyya, kuma ba za mu karɓe su ba. Sun ci amanar jam’iyya. Ba shi da ƙarfin da zai iya ƙalubalantar Tinubu,“ in ji Major.

Sai dai ya amince cewa Kwankwaso yana da ‘yancin tsayawa takara, amma ya ce bai kamata ya jawo jam’iyyar NNPP rikici ba.

“Muna da masu sha’awar tsayawa takara a 2027, kuma za mu bi doka da tsarin jam’iyya wajen fitar da ɗan takara,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci ’yan Najeriya da kada su saurari maganganun ’yan Kwankwasiyya.

“Kwankwaso ya kafa tasa jam’iyyar idan yana da muradin yin takara. NNPP ta wuce wannan matakin, ba za mu mayar da hankali kan rigingimun banza ba,” a cewar Dokta Major.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum
  • Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba
  • Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPP
  • An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?
  • Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur