Mataimakin shugaban kasar Iran na Farko ya ce; Al’ummar Imam Husaini a Iran ba za su bari makiya su cimma mummunan burinsu ba

Mataimakin shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran na farko Muhammad Reza Aref ya rubuta a cikin wata wasika cewa: Domin kare martabar Iran da kasar al’ummar Imam Husaini a Iran da zuciya daya da murya daya da hadin kan al’umma ba za su taba barin mafarkin masu kyama ya tabbata ba.

Aref ya wallafa wani faifan bidiyo a shafinsa na Instagram a jajibirin ranar Ashura inda ya rubuta cewa: “Saboda Iran da kasar da tushen al’ummar Mabiya Imam Husaini a Iran da zuciya daya da murya daya da hadin kan al’umma ba za su taba bari mafarkin makiya ya tabbata ba.

A yammacin jiya Asabar ne Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya halarci zaman juyayin Ashura, domin tunawa da shahadar Imam Husaini (a.s).

A daidai lokacin da ake gudanar raya daren jajibirin ranar Ashura, an gudanar da zaman makoki a Husainiyar Imam Khumaini (Allah ya tsarkake ruhinsa) tare da halartar jagoran juyin juya halin Musulunci Imam Khamenei da dimbin jama’a daga bangarori daban-daban na al’umma.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kassim  ya mayar da martani ga wadanda suke son, kungiyar ta mika makamanta, yana mai cewa; Ku fara da neman makiya su fice daga cikin Lebanon, domin babu hankali ace ba ku cewa komai akan ‘yan mamaya,ya zamana kuna neman wanda yake gwgawarmaya ya ajiye makamansa.”

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Duk wanda ya amince da mika wuya, ya yi, amma mu ba za mu laminta da hakan ba. Mu almajiran makarantar Imam Hussain ( a.s) ne da yake cewa: Ba Za Mu Taba Lamunta Da Kaskanci Ba.”

Sheikh Na’im Kassam ya ce: Wadanda suke jingina da kasashen waje, suna kuskuren lissafi, domin masu gwgawarmaya ba su ganin wani kwarjinin abokan gaba, ba kuma za su sarayar da hakkokinsu ba.”

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa: Babban ci gaba na hakika da aka samu shi ne ‘yanto da kasa, muna kuma cikin Shirin ci gaba da yin haka a kodayaushe.”

Sheikh Na’im Kassim ya jaddada cewa;raya lokacin shahadar Imam Hussain ( a.s),  raya musulunci ne da dukkanin bangarorinsa, da kuma manhajarsa.

 Haka nan kuma ya ce; Musulunci wanda Imam Hussian ( a,s) da iyalan gidansa su ka kare shi, shi ne fidirar mutum tabbatacciya, yana kuna ayyana nauyin da ya rataya akan kowance mutum daidai da gwargwadon dabi’arsa ta namiji ko mace. Nauyin da ya rataya a wuyan namiji shi ne daukar makami domin yin yaki na bayar da kariya, ita kuwa mace ba a dora mata yin hakan ba,amma a lokaci daya abokiyar tarayya ce a cikin jihadi ta hanyar rawar da take takawa a bayan fagen daga, da su ka hada yin tarbiyya da ayyukan da muhimmancinsu bai gaza na namiji a fagen daga ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Iran ta Bukaci Gudanar da Bincike Kan Sacewar jami’ar Diblomasiyyar kasar A Lebanon Shekaru 43 Da Suka gabata
  •  Maduro Ya Jinjina Wa Jagororin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  •  Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Ayatullahi Khatami Ya Ce Hukuncin Da Ya Cancanci Trump Da Netanyahu Shi Ne Kisa Saboda Zubar Da Jinin Bil’Adama
  •  A Yau Juma’a Ne Ake Gudanar Da Taron Karrama Shahid Birgediya Janar Husain Salami A Nan Birnin Tehran