Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha
Published: 6th, July 2025 GMT
Majalisar Dattawan Nijeriya ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha Akpoti Uduaghan gabanin cikar wa’adin dakatar da ita da ta yi tsawon watanni shida.
Majalisar ta ce ala tilas ne dakatacciyar Sanatar ta bayar da hakuri tare da neman afuwa a hukumance gabanin cika umarnin da ta wata Babbar Kotun Tarayya ta bayar na dawo da ita.
Shugaban Kwamitin Labarai da Harkokin Jamaa na Majalisar Dattawa, Sanata Adeyemi Adaramodu ne ya bayyana hakan yayin da yake martani kan hukuncin da kotun ta yanke a kan Sanata Natasha.
Ya yi bayanin cewa, a yayin yanke hukuncin da ta bayar da umarnin dawo da Sanata Natasha, kotun ba ta hana majalisar ladabtar da mambobinta a yayin da ta same su da laifi kamar yadda yake a cikin kundin tsarinta.
A bayan nan ne dai wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta buƙaci Majalisar Dattawan ta dawo da Sanata Natasha Akpoti.
Da take yanke hukunci, Mai Shari’a Binta Nyako ta kwatanta cewa dakatar da Natasha tsawon watanni shida da aka yi, ya yi tsauri.
Kotun ta kuma ce Shugaban Majalisar Dattawan Godswill Akpabio bai yi laifi ba, lokacin da ya hana Natasha yin magana a majalisa saboda lokacin ba ta zauna kan ainihin kujerar da aka ware mata ba.
Ta kuma buƙaci Sanata Natasha ta bai wa majalisar hakuri.
Sai dai a cewar kotun, tun da ’yan majalisa suna da tsawon kwanaki 181 don zama a kowane zango, dakatar da Natasha tsawon watanni da aka yi — yana kamar hana ta aiwatar da haƙƙokinta ne ga ’yan mazaɓarta na tsawon kwanaki 180.
Har ila yau, kotun ta ce Majalisar Dattawa tana da damar hukunta kowane ɗan majalisa da ya yi laifi, sai dai kada hukuncin ya yi tsaurin da zai hana aiwatar da ayyukan mazaɓar ɗan majalisa da aka dakatar.
Mai Shari’a Nyako ta kuma kori batun da Akpabio ya gabatar cewa kotun ba ta hurumin sauraron ƙarar.
Tun da farko, kotun ta ci Sanata Natasha tarar naira miliyan biyar saboda raina kotu, wanda ya hana ɓangarorin biyu yin magana a bainar jama’a kan batun.
Ta kuma buƙaci Natasha ta nemi afuwa a gidajen jaridu biyu da shafinta na Facebook cikin kwanaki bakwai.
A watan Maris ne Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha bayan da ta zargi Sanata Godswill Akpabio da cin zarafi na lalata, laifin da har yanzu ya musanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: dawo da Sanata Natasha Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Folasade Boriowo, ya fitar, ta ce a karon farko cikin shekaru da dama, daliban Nijeriya za su ci gaba da karatun tarihin Nijeriya tun daga Firamare 1 zuwa karamar Sakandare 3 yayin da daliban SSS 1 – 3 za su koyi sabon darasin da aka samar na ‘Civic and Heritage Studies’, wanda ya hada tarihin Nijeriya da Ilimin zamantakewar Jama’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp