Leadership News Hausa:
2025-12-02@10:00:54 GMT

Ga Dukkan Alamu Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Published: 17th, March 2025 GMT

Ga Dukkan Alamu Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

A ranar Larabar da ta gabata ne, harajin kashi 25 na shugaban Amurka Donald Trump kan duk wasu kayayyakin karafa da goron ruwa ya fara aiki. Inda Kanada ta mayar da martani kai tsaye da harajin kashi 25 kan kayayyakin Amurka na sama da dala biliyan 20, wadanda suka hada da karafa, kwamfutoci da kayan wasanni.

EU ita ma mayar da martani da haraji kan kayayyakin Amurka na kusan dala biliyan 28, wanda zai fara aiki a ranar 13 ga Afrilu.

Hasashen dake tattare da manufar Trump shi ne, idan farashin kayayyakin da ake shigowa da su daga kasashen waje ya tashi a dalilin karin haraji, to za a maida hankali kan kafa masana’antun cikin gida dake samar da irin wadannan kayayyaki, ta hakan za a samu karin ayyukan yi a Amurka. Sai dai Trump ya manta cewa, tsarin karin harjin kwastam na iya zama takobi mai kaifi biyu idan aka yi amfani da shi ba bisa ka’ida ba, kuma zai iya raunata wanda ke rike da shi. Wannan takobin a hannun Trump, yana barazanar zama “makamin lalata huldar cinikayya tsakanin kasa da kasa,” yayin da hakan ke mummunan tasiri ga tattalin arzikin Amurka.

Layin Dogo Na Habasha-Djibouti Na Habaka Kasuwanci Da Karfafa Hada-hadar Kayayyaki  Gwamnatin Kano Ta Umarci Ma’aikatanta Da Su Tantance Allbashin Watan Maris Kafin A Biya Su

Sanin kowa ne cewa Amurka ba za ta iya farfado da tsarin samar da kayayyaki da masana’antunta da suka dade da bacewa a cikin dare guda ba, zai dauki watanni ko ma shekaru kafin a sake fasalin tsarin samar da kayayyaki da masana’antunta, duk da cewa masu sayayya na Amurka sun riga sun tsunduma cikin matsalar hauhawar farashin kayayyaki na yau da kullum, sakamakon matakin kara haraji na Trump.

Bisa ka’ida, Trump yana da shekaru hudu ya cimma manufarsa, amma a aikace, lokacin ya yi kadan da zai gamsar da masu sayayya na Amurka. Idan har wannan manufar ta ci gaba da kasancewa a cikin watanni masu zuwa, to tabbas jama’a za su janye goyon bayansu ga shugaban, hatta a tsakanin ‘yan jam’iyyar Republican Congress, wadanda ya dogara da su wajen aiwatar da sabbin dokoki. Idan har suna ganin damar saken zabarsu na cikin hadari a zaben tsakiyar wa’adi na badi saboda tsarin tsuke bakin aljihu da matakin kara kudin fito da ya aiwatar, za su iya yin watsi da goyon bayan da suke baiwa shirin shugaban kasar. Tuni dai ana samun karuwar damuwa daga ’yan kasuwa, musamman wadanda suka dogara da tsarin samar da kayayyaki na duniya wanda manufar kudin fito ta Trump ta kawo ma cikas. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 

’Yan bindiga sun yi garkuwa da wani fasto da matarsa da mabiyansa a yayin da suke tsaka da ibada a coci da ke a  Jihar Kogi.

Wani ganau da ke cikin cocin a lokacin da aka kai harin, Adegboyega Ogun, ya ce misalin ƙarfe 9.30 na safe ’yan bindigar suka kai harin suna bude wuta.

“Mutane sun qarshe ta ko’ina, har da faston, wanda aka fi sani da Baba Orlando da matarsa da wasu masu ibada duk an yi garkuwa da su. Gaskiya harin ya yi muni, dukkanmu tserewa muka yi daga cocin.”

Sace masu ibadar a ranar Lahadi a Cocin Cherubim and Seraphim ya auku ne bayan a kwanan nan Gwamna Usman Ododo, ya koka da cewa wasu  manyan jagororin ’yan bindiga sun dawo jihar.

Kafin nan a ranar Asabar ’yan bindiga sun tare hanya, suka yi garkuwa da matafiya cikin motoci uku a kan hanyar Isanlu-MakutuIdofin da ke Ƙaramar Hukumar Yagba ta Gabas.

Wani mazaunin yankin, Enimola Daramola ya bayyana cewa, “mutum ɗaya ne kacal ya samu tserewa a motocin da aka tafi da su cikin daji.”

“Amma mun samu labari yau cewa sojoji da ’yan banga sun bi sawun ’yan bindigar inda suka yi musayar wuta suka ceto wasu daga cikin mutanen,”

A ranar Lahadi kuma aka samu rahoton cewa an kai wa wata motar haya hari.

“Matuƙin motar da fasinjojin sun tsallake rijiya da baya. Yanzu hanyar ta zama mai hatsari sosai,” in ji David Juwon, mazaunin yankin Isanlu.

Sabon harin Cocin Cherubim and Seraphim na zuwa ne makonni kaɗan bayan makarancinsa da ’yan bindiga suka sace mutane 38 a wani Cocin CAC da ke yankin Eruku na Karamar Hukumar Ekiti a Jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran ‘Yan Democrat a Majalisar Dattawa: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela
  • Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala
  • Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku
  • Iran: Kalaman Da Trump Yayi Na Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venuzuwela Ya Sabama Doka.
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163