Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe
Published: 6th, July 2025 GMT
Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya gargaɗi sarakunan gargajiya a faɗin ƙananan hukumomi 11 na jihar kan zargin hannu a mamaye hanyoyin kiwo da filayen kiwo, abin da ke haddasa rikici tsakanin makiyaya da manoma.
Gwamnan ya nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa wasu sarakuna na karɓar cin hanci suna kuma ba da damar shiga filayen kiwo ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ke ƙara tayar da zaune tsaye a tsakanin al’umma.
“Duk wanda aka kama yana da hannu a wannan aika-aikar, za mu hukunta shi bisa doka,” in ji Gwamna.
Ya kuma roƙi makiyaya da su guji shiga gonaki domin hakan na haifar da rikici maras amfani.
Ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta aiwatar da shawarwarin kwamitin da ke bincike kan lamarin, tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa ta hanyar kare hanyoyin kiwo da tabbatar da adalci wajen amfani da filaye.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Filaye jihar Gombe Sarakuna
এছাড়াও পড়ুন:
Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
Gidajen mai da dam aka rufe, yayin da wadanda suka kasance da dan sauran mai kuma, layuka ne marasa iyaka suka makare su, lamarin da ta kai har kwana mutane ke yi a gidajen man.
A kan titunan babban birnin kasar, bayanai sun ce ba kasafai ake ganin motoci suna kai komo ba, ko kuma mutane na tura babura, bisa alama dai mutane sun ajiye ababen hawansu a gida.
Sai dai duk da wannan karancin man da ake fama da shi, farashinsa ya ci gaba da kasancewa a yanda yake, domin kuwa farashin lita na mai CFA 775 yayin da dizal yake akan CFA 725.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA