Aminiya:
2025-07-06@16:33:13 GMT

Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe

Published: 6th, July 2025 GMT

Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya gargaɗi sarakunan gargajiya a faɗin ƙananan hukumomi 11 na jihar kan zargin hannu a mamaye hanyoyin kiwo da filayen kiwo, abin da ke haddasa rikici tsakanin makiyaya da manoma.

Gwamnan ya nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa wasu sarakuna na karɓar cin hanci suna kuma ba da damar shiga filayen kiwo ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ke ƙara tayar da zaune tsaye a tsakanin al’umma.

Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka

“Duk wanda aka kama yana da hannu a wannan aika-aikar, za mu hukunta shi bisa doka,” in ji Gwamna.

Ya kuma roƙi makiyaya da su guji shiga gonaki domin hakan na haifar da rikici maras amfani.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta aiwatar da shawarwarin kwamitin da ke bincike kan lamarin, tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa ta hanyar kare hanyoyin kiwo da tabbatar da adalci wajen amfani da filaye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Filaye jihar Gombe Sarakuna

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum
  • Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
  • Majalisar Jihar Jigawa Ta Bukaci Karamar Hukumar Roni Ta Samar Da Karin Ajujuwa Ga Fulani Makiyaya
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
  • Ambaliya da iska sun lalata gidaje 171 a Gombe — SEMA
  • ’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA