Mutun 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano
Published: 6th, July 2025 GMT
Aƙalla mutum 21 ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babban titin Zariya zuwa Kano, kamar yadda Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), ta tabbatar.
Hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 8:23 na safe a unguwar Kasuwar Dogo da ke yankin Dakatsalle.
Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a GombeHatsarin ya rutsa da wata babbar mota ƙirar DAF mai lambar GWL 422 ZE da kuma motar ɗaukar fasinjoji ƙirar Toyota Hummer mai lambar KMC 171 YM.
FRSC, ta ce bincike ya nuna cewa direban motar fasinjojin ne ya karya doka ta hanyar bin hanyar da ba ta dace ba, wanda hakan ya sa suka yi karo da babbar motar.
Bayan aukuwar hatsarin, motocin biyu sun kama da wuta, inda mutane da dama suka ƙone ƙurmus.
Kwamandan FRSC na Kano, MB Bature, ya ce jami’ansu sun isa wajen cikin gaggawa bayan samun rahoto.
Sun kuma kira ma’aikatan kashe gobara na jihar da na tarayya domin kashe gobarar da kuma ceto waɗanda hatsarin ya rutsa da su.
Mai magana da yawun FRSC, Abdullahi Labaran, ya ce: “Mutum 24 ne hatsarin ya rutsa da su. Abin takaici, 21 sun rasu, yayin da uku suka jikkata.”
Gawarwakin da suka ƙone an kai su ɗakin ajiye gawa na Asibitin Nassarawa da ke Kano, yayin da waɗanda suka jikkata ke samun kulawa a Asibitin Gwamnati da ke Garun Malam.
Bayan haka, jami’an FRSC tare da taimakon ’yan sanda sun ɗauke motocin da suka tare hanya domin sauƙaƙa zirga-zirgar ababen hawa a titin.
Kwamanda Bature, ya bayyana alhininsa kan wannan mummunan lamari, tare da miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu.
Ya kuma yi wa waɗanda suka jikkata addu’ar samun sauƙi.
Ya kuma yi amfani da wannan dama wajen jan hankalin direbobi su guji karya doka; kamar bin hanya ba daidai ba da tuƙin ganganci, wanda hakan ke haddasa haɗura.
“Wannan lamari abin takaici ne wanda ke nuna muhimmancin bin ƙa’idojin hanya. Mafi yawan haɗura za a iya kauce musu idan direbobi za su kiyaye doka,” in ji Bature.
Ya kuma buƙaci direbobi, musamman na motocin haya, da su guji gudu fiye da ƙima da ganganci a hanya, wanda a cewarsa shi ne babban dalilin da ke haddasa haɗura da asarar rayuka.
Ga hotunan yadda hatsarin ya auku:
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin mota Zariya hatsarin ya
এছাড়াও পড়ুন:
Sakin Maryam Sanda shi ne ƙololuwar zalunci —Dangin Bilyaminu
Dangin Marigayi Bilyaminu Ahmed Bello sun bayyana takaicinsu bisa sanya matarsa, Maryam Sanda, wadda kotu ta ɗaure ta kan laifin soka masa wuka har lahira, a cikin jerin mutanen da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa afuwa.
A shekarar 2020 ne kotu ta yanke wa Maryam Sanda hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun ta da laifin kashe mijinta Bilyaminu.
Sanarwar da dangin marigayin suka fitar ɗauke da sa hannun Dakta Bello Haliru Mohammed (Dangaladiman Gwandu) ta bayyana afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda a matsayin “mummunan famu,” da kuma ƙololuwar rashin adalci ga ɗan uwansu.
Sun bayyana takaici bisa sakin Maryam Sanda daga gidan yari, wanda suka kira da neman faranta wa danginta rai, ba tare da la’akari da rabi na har abada da ta yi wa ’yan uwa da iyaye da dangi da a aminan Bilyaminu da kashe ba.
Maryam Sanda mai shekara 37 tana daga cikin jerin mutane 175 da Shugaba ya yi wa afuwa a ranar Alhamis da ta gabata.
Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila Issa Bakary Tchiroma ne ya lashe zaɓen Kamaru —’Yan adawaLaifukan da aka yanke musu hukunci su haɗa da cin amanar ƙasa, kisan kai, da masu sayar da makamai ga ’yan ta’adda da masu garkuwa da mutane da dillalan miyagun ƙwayoyi da ’yan damfara da masu haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.
Sanarwar da kakakin Shugaban Ƙasa Bayo Onanuga ya fitar ta nuna cikinsu akwai masu zaman rai da rai da aka yi wa afuwa gaba ɗaya da waɗanda aka sassauta hukuncin.
Akwai kuma wadanda aka yi wa afuwa bayan ransu kamar Manjo-Janar Mamman Vatsa da Cin Herbert Macaulay da Ken Saro Wiwa, da fitattun mutane irin su Farfesa Wole Soyinka da Faruk Lawan da Farfesa Magaji Garba da Manjo Akubo da sauransu.
Jerin sunayen mutanen da aka yi afuwar ya haifar da ce-ce-ku-ce. Onanuga ya ce an yi musu afuwa ne bayan sun nuna nadama tare da zama mutanen kirki gami da yawan shekaru da sauransu.
Shari’ar Maryam SandaDambarwar Maryam Sanda yana daga cikin shari’o’in rikicin ma’aurata da ya kai ga kisa suka fi ɗaukar hankali a baya-bayan nan.
Abin ya faro ne bayan rikici tsakaninta da Bilyaminu wanda a ƙarshe ta soka masa wuƙa har lahira.
Ta musanta tuhumar da ake mata, a ayin da aka gurfanar da ita a gaban Babbar Kotun Abuja.
Bayan tsawon lokaci ana shari’a, a watan Disambar 2020, Mai Shari’a Yusuf Halilu, na Kotun Ɗaukaka Ƙara yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya, wanda daga baya Kotun Koli ta tabbatar a watan Oktoba 2023.
Daga lokacin zuwa yanzu ta yi zaman shekara shida da wata takwas a Babban Gidan Yarin Suleja.
Martanin dangin BilyaminuDangin Bilyaminu sun bayyana sakin Maryam Sanda a matsayin “rashin adalci mafi raɗaɗi da za a iya jefa iyali saboda wanda suke ƙauna,” inda suka bayyana ta a matsayin “mai kisa da kotu ta tabbatar da laifinta” wadda ba ta taɓa nuna nadama ba tun daga farkon shari’arta har zuwa ƙarar da ta daukaka.
Sun ce tun bayan mummunan abin da ya faru a ranar 19 ga Nuwamba, 2017, sun zabi su yi shiru saboda girmama ’ya’yan da aka bari, duk da ƙaryar ɓangarenta ake yaɗawa.
Sun bayyana cewa sun dogara ne da tsarin shari’a, wanda ya tabbatar da hukuncin kisa da kotunan farko suka yanke — har zuwa Kotun Koli a 2023.
Iyalin sun ce wannan hukunci ya ba su ɗan nutsuwa, amma yafiyar shugaban ƙasa ta sake buɗe musu raunin da ke ci gaba da zubar da jini, tare da rage darajar rayuwar wanda aka kashe. Sun soki dalilan yafiyar, suna cewa an yi ta ne bisa roƙon iyalan Sanda, alhali kuwa Bilyaminu ma ɗa ne, aboki, kuma uba mai ƙauna wanda “aka tauye masa damar rayuwa da renon ’ya’yansa.”
Sun kammala da cewa sun bar komai ga adalcin Allah, “Mai Shari’a na gaskiya,” tare da yin addu’a ga Allah Ya jikan Bilyaminu, Ya kuma ba ’ya’yansa da masoyansa ƙarfin jure wannan raɗaɗin.