Leadership News Hausa:
2025-07-08@06:14:07 GMT

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Published: 17th, March 2025 GMT

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Bari ma in yi waiwaye. In yi bi-ta-da-ƙulli. Da jihohin Arewa na musulmi suke yin hutun lahadi ba su zuwa aiki to don su je gidan uban wane ne? A Katsina dai wannan ba zagi ne ba. A maye gurbinsa da hutun Juma’a ranar zuwa sallar Juma’a. Ranar Idi ce. Da ake yin hutu lokacin kirsimati ko wata Ista shi kuma hutun menene ne? Har yanzu Turawan na nan ne? Idan aka ce a yi hutu lokacin da yara ke taya iyayensu aiki a gona za su gane hikimar wannan tunda abinci zai zo gida.

Lokaci ya yi da musulmi za su nuna wa duk wani mai shishshigi da takalar faɗa yatsa. Tsarin dimokuraɗiyya tsari ne na masu rinjaye a majalisa, su yi doka ta dace da mutane ma fi rinjaye. Ko musulmin Abiya ko Kuros Ribas sun nemi a ba ƴaƴansu hutu domin azumi?

A yi amfani da hutun a yi karatu, karatun ilmi na haƙiƙa. Da ‘yan bokon da ke mulki sun je makarantar Ramadan sun sauke kamar yadda suka je sakandare suka gama, wasu ma har sun je jami’a da ba su zama ɓarayi a ofis ba.

Da ba a riƙa tallata su a talabijin sun yi laya da biliyoyi ba. Da ba mu ga uba da dansa ba a gaban alkali ana cewa ku ɓarayi ne suna musu har lauyoyinsu na shedar zur. A sha ruwa lafiya

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

An fara tuhumar tsohon ɗan ƙwallon Arsenal, Thomas Partey da laifuka biyar da suka haɗa da fyaɗe da kuma cin zarafi, an bayar da rahoton cewa ya aikata laifukan ne a tsakanin shekarar 2021-2022, cewar ‘yansandan Birtaniyya.

Daga cikin laifukan akwai fyaɗe akan wasu mata uku waɗanda ake tuhumarsa da cin zarafinsu ta hanyar tursasawa kan mace ta farko da ta biyu sai kuma laifin lalata da mace ta uku.

‘Yansanda a ƙasar Birtaniya sun ce ya kamata Thomas ya bayyana a Kotun Majistare ta Westminster a ranar 5 ga watan Agusta, tuhumar ta biyo bayan binciken da jami’an tsaro suka gudanar, wanda ya fara a watan Fabrairun 2022 bayan da ‘yansanda sun samu rahoton fyaɗen.

Partey dai ya bar Arsenal bayan kwantiraginsa ya ƙare, kuma an ce ƙungiyoyin da suka haɗa da Juventus da Barcelona da kuma Fenerbahce suna zawarcinsa, ɗan wasan na Ghana ya kasance a Emirates na tsawon shekaru biyar bayan an siyo shi daga Atletico Madrid, kuma ya buga wa ƙasarsa wasanni da dama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
  • China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS
  • Trump Ya Yi Barazanar Ƙarin Haraji Ga Ƙasashen Da Suka Rungumi BRICS
  • AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
  • Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
  • ‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila