Aminiya:
2025-07-12@08:50:01 GMT

Mahaifina ne kaɗai shugaban da bai damu ya azurta kansa ba — Seyi Tinubu

Published: 17th, March 2025 GMT

Seyi Tinubu, ɗan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa, mahaifinsa ne kaɗai shugaban ƙasar da ba shi da burin azurta kansa da kuɗin talakawa.

Har wa yau ya ƙara da cewa shi kaɗai ne shugaban da ke bai wa matasa damammaki a gwamnatinsa.

Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa

Seyi ya faɗi hakan ne yayin yi wa wani dandazon matasa jawabi a Yola, babban birnin Jihad Adamawa.

Seyi Tinubu wanda ke ci gaba da shawagi a wasu jihohin ƙasar yana buɗa-baki, ya ce a kwanakin wasu sun dage wajen sukar mahaifinsa, sai dai hakan ba zai sa ya yi ƙasa a gwiwa ba wajen kawo ci gaba a Nijeriya.

Har wa yau, Seyi ya ce mahaifinsa ne kaɗai ne shugaban da ya samar da yanayin tattalin arziki da kowa ke amfana a ƙasar a halin yanzu.

“Shi kaɗai ne shugaban ƙasar da ba shi wata manufa ko burin azurta kansa.”

A bayan nan ne tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya zargi Gwamnatin Tinubu da rashawa.

Cikin sabon littafin da ya ƙaddamar yayin bikin cikarsa shekaru 88, Obasanjo ya caccaki Gwamnatin Tinubu kan abin da ya kira ɓarna da almubazzaranci musamman dangane da yadda ta kashe kimanin Naira biliyan 21 wajen gina wa Mataimakin Shugaban Kasa katafaren gida.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya gana a yau Juma’a da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio a Kuala Lumpur na Malaysia, inda suka yi musayar ra’ayi kan danganatkar Sin da Amurka da batutuwan dake jan hankalin kasashensu.

Wang Yi ya yi cikakken bayani kan matsayar Sin game da raya dangantakarta da Amurka, yana mai nanata bukatar bangarorin biyu su aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen suka cimma zuwa manufofi da ayyuka na hakika. Ya ce fatan ita ce Amurka ta kalli Sin da ra’ayi na sanin ya kamata da tsara manufar hulda da Sin bisa burin zaman lafiya da hadin gwiwar moriyar juna da tafiyar da dangantakarta da Sin bisa matsayi na daidaito da girmamawa da moriyar juna, tare da hada hannu da Sin wajen lalubo hanya mai dacewa da za su yi mu’amala ta fahimtar juna a sabon zamani.

Bangarorin biyu sun amince cewa, ganawar ta su ta yi ma’ana, kuma za su karfafa hanyoyin diplomasiyya na tuntubar juna da tattaunawa a dukkan matakai da bangarori, da ba sassan diplomasiyya masu kula da raya dangantakar kasashen biyu damar taka rawar da ta kamata da lalubo bangarorin fadada hadin gwiwarsu yayin da suke hakuri da bambance-bambancen dake tsakaninsu. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
  • Malaman Jihar Jigawa Sun Karrama Shugaban Hukumar Alhazai Ta Jihar
  • Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Jagora Da Kansa Ya Shiga Dakin Ba Da Umarnin Sojin Lokacin Yaki
  • Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
  • Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN
  • Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa