Aminiya:
2025-12-13@08:00:37 GMT

Mahaifina ne kaɗai shugaban da bai damu ya azurta kansa ba — Seyi Tinubu

Published: 17th, March 2025 GMT

Seyi Tinubu, ɗan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa, mahaifinsa ne kaɗai shugaban ƙasar da ba shi da burin azurta kansa da kuɗin talakawa.

Har wa yau ya ƙara da cewa shi kaɗai ne shugaban da ke bai wa matasa damammaki a gwamnatinsa.

Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa

Seyi ya faɗi hakan ne yayin yi wa wani dandazon matasa jawabi a Yola, babban birnin Jihad Adamawa.

Seyi Tinubu wanda ke ci gaba da shawagi a wasu jihohin ƙasar yana buɗa-baki, ya ce a kwanakin wasu sun dage wajen sukar mahaifinsa, sai dai hakan ba zai sa ya yi ƙasa a gwiwa ba wajen kawo ci gaba a Nijeriya.

Har wa yau, Seyi ya ce mahaifinsa ne kaɗai ne shugaban da ya samar da yanayin tattalin arziki da kowa ke amfana a ƙasar a halin yanzu.

“Shi kaɗai ne shugaban ƙasar da ba shi wata manufa ko burin azurta kansa.”

A bayan nan ne tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya zargi Gwamnatin Tinubu da rashawa.

Cikin sabon littafin da ya ƙaddamar yayin bikin cikarsa shekaru 88, Obasanjo ya caccaki Gwamnatin Tinubu kan abin da ya kira ɓarna da almubazzaranci musamman dangane da yadda ta kashe kimanin Naira biliyan 21 wajen gina wa Mataimakin Shugaban Kasa katafaren gida.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”

Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”

Masana a Taron Abuja na Tattaunawa kan Tattalin Arziki Kasa da ake wa lakabi da Abuja Economic Dialogue 2025 da Kamfanin Ignite Capital ke shiryawa duk shekara da haxin gwiwar Kamfanin Innovision Global Consulting sun yi hasashen cewa, za a samu saukar kayan masarufi da Karuwar samar da ayyukan yi a faxin kasa a shekara mai zuwa ta 2026.

Masana tattalin arzikin da suka yi fashin baki kan yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a cikin watanni tara da suka gabata, a taro sun haxa da Dakta Paul Arinze, Shugaban Kamfanin Bincike da Nazari kan harkokin tattalin arziki mai suna Pedestal Africa da Dakta Umar Kwairanga Kwararre kan harkokin tattalin arziki da ayyukan banki da Dakta Sara Alade tsohuwar Mataimakiyar Gwamnan Babban Banki na Kasa kuma Kwararriya a fagen tattalin arziki da kuma Dakta Nuruddeen Zauru wani masanin tattalin arziki.

A cikin sakonsa na fatan alheri tsohon Mataimaki Shugaban Kasa kuma Sardaunan Zazzau, Alhaji Namadi Sambo ya yi tsokaci kan bukatar cewa, lokaci ya yi da gwamnati za ta xauke cigaban da take ikirarin samu a fannin tattalin arziki daga alkalumma a takarda zuwa aiwatarwa a aikace. Ta yadda talakawa za su ga sauKin da ci gaban da aka samu kasa ba labari ba.

Da yake tofa albarkacin bakinsa a taron tsohon Shugaban Majalisar Dattawa ta Qasa, Alhaji Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu ya dace shugabanni a Nijeriya su san cewa, ba tare da samar da cikakken tsaro da dauwamammiyar wutar lantarki ba tattalin arzikin Nigeriya zai ci gaba da yin kwan gaba-kwan baya.

Saraki ya kuma yi kira da gwamnati da rinka karfafa gwiwar kamfanonin cikin kasa ta hanyar sayen kayayyakin da suke samarwa.

Mai masaukin baki kuma Shugaban Kamfani Ignite Capital, Bukar Abba Kyari ya yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu, kan irin matakan da yake xauka don inganta tattalin arzikin kasa tare da tallafa wa matasa kan harkokin da suka shafi kasuwancin zamani na yanar gizo.

 

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin