Mahaifina ne kaɗai shugaban da bai damu ya azurta kansa ba — Seyi Tinubu
Published: 17th, March 2025 GMT
Seyi Tinubu, ɗan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa, mahaifinsa ne kaɗai shugaban ƙasar da ba shi da burin azurta kansa da kuɗin talakawa.
Har wa yau ya ƙara da cewa shi kaɗai ne shugaban da ke bai wa matasa damammaki a gwamnatinsa.
Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a AdamawaSeyi ya faɗi hakan ne yayin yi wa wani dandazon matasa jawabi a Yola, babban birnin Jihad Adamawa.
Seyi Tinubu wanda ke ci gaba da shawagi a wasu jihohin ƙasar yana buɗa-baki, ya ce a kwanakin wasu sun dage wajen sukar mahaifinsa, sai dai hakan ba zai sa ya yi ƙasa a gwiwa ba wajen kawo ci gaba a Nijeriya.
Har wa yau, Seyi ya ce mahaifinsa ne kaɗai ne shugaban da ya samar da yanayin tattalin arziki da kowa ke amfana a ƙasar a halin yanzu.
“Shi kaɗai ne shugaban ƙasar da ba shi wata manufa ko burin azurta kansa.”
A bayan nan ne tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya zargi Gwamnatin Tinubu da rashawa.
Cikin sabon littafin da ya ƙaddamar yayin bikin cikarsa shekaru 88, Obasanjo ya caccaki Gwamnatin Tinubu kan abin da ya kira ɓarna da almubazzaranci musamman dangane da yadda ta kashe kimanin Naira biliyan 21 wajen gina wa Mataimakin Shugaban Kasa katafaren gida.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati
Hukumar Kula da Rajistar Kamfanoni (CAC) ta ba wa dukkan masu gudanar da harkar kuɗi ta PoS a fadin Najeriya, wa’adin ranar 1 ga Janairu, 2026, su yi cikakken rajista ko ta rufe su.
A ranar Asabar, Hukumar ta sanar cewa yawaitar masu PoS marasa rajista a sassan ƙasar nan ya yawaita. Don haka ta jaddada cewa gudanar da PoS ba tare da rajista ba ya saɓa wa Dokar Kamfanoni ta 2020 da kuma ka’idojin Babban Bankin Najeriya (CBN).
Hukumar ta kuma zargi wasu kamfanonin fasahar kudi (fintech) da daukar wakilai ba tare da rajista ba, tana bayyana wannan dabi’a a matsayin da sakaci kulawa da kuma barazana ga daidaiton tsarin kuɗi na ƙasar.
Ta ce hakan na jefa miliyoyin ’yan Najeriya, ciki har da ’yan kasuwa ƙanana da masu aiki a karkara, cikin haɗarin tattalin arziki da asarar jari.
Ɗa da mahaifi sun mutu a cikin rijiya a Kano Ƙasashen waje na taimaka wa ’yan ta’adda a Najeriya —Sheikh Gumi“Duk fintech da ke ba da damar ayyukan da ba bisa ƙa’ida ba za a saka su cikin jerin waɗanda ake sa wa ido, sannan za a kai rahotonsu ga CBN. Duk masu PoS an umurce su da su yi rajista nan da nan. Bin doka wajibi ne.
“Daga ranar 1 ga Janairu, 2026, ba wani mai PoS da zai ci gaba da aiki a Najeriya ba tare da cikakken rajista ba,” in ji CAC.
Wannan daiba shi ne karo na farko da aka yi kira kan buƙatar tsaurara dokokin sa ido kan harkar PoS ba.
An sha yin kira ga CBN da ya ɗauki matakan gaggawa wajen daƙile yawaitar damfara da ke addabar harkar PoS a faɗin ƙasar.