Aminiya:
2025-12-12@04:41:46 GMT

Mahaifina ne kaɗai shugaban da bai damu ya azurta kansa ba — Seyi Tinubu

Published: 17th, March 2025 GMT

Seyi Tinubu, ɗan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa, mahaifinsa ne kaɗai shugaban ƙasar da ba shi da burin azurta kansa da kuɗin talakawa.

Har wa yau ya ƙara da cewa shi kaɗai ne shugaban da ke bai wa matasa damammaki a gwamnatinsa.

Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa

Seyi ya faɗi hakan ne yayin yi wa wani dandazon matasa jawabi a Yola, babban birnin Jihad Adamawa.

Seyi Tinubu wanda ke ci gaba da shawagi a wasu jihohin ƙasar yana buɗa-baki, ya ce a kwanakin wasu sun dage wajen sukar mahaifinsa, sai dai hakan ba zai sa ya yi ƙasa a gwiwa ba wajen kawo ci gaba a Nijeriya.

Har wa yau, Seyi ya ce mahaifinsa ne kaɗai ne shugaban da ya samar da yanayin tattalin arziki da kowa ke amfana a ƙasar a halin yanzu.

“Shi kaɗai ne shugaban ƙasar da ba shi wata manufa ko burin azurta kansa.”

A bayan nan ne tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya zargi Gwamnatin Tinubu da rashawa.

Cikin sabon littafin da ya ƙaddamar yayin bikin cikarsa shekaru 88, Obasanjo ya caccaki Gwamnatin Tinubu kan abin da ya kira ɓarna da almubazzaranci musamman dangane da yadda ta kashe kimanin Naira biliyan 21 wajen gina wa Mataimakin Shugaban Kasa katafaren gida.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro

Gwamnatin Tarayyar Najeriya da Masarautar Saudiyya sun sanya hannu kan wata sabuwar yarjejeniya domin ƙarfafa dangantakar tsaro da haɗin gwiwar soja tsakanin ƙasashen biyu.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle kan yaɗa labarai Ahmed Dan Wudil ya fitar, ta bayyana cewa yarjejeniyar za ta shafi muhimman fannoni kamar musayar bayanan leƙen asiri, horas da sojoji, haɗin gwiwa a harkar samar da kayan yaki da kuma gudanar da ayyukan tsaro tare.

Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana

Minista Matawalle ne ya sanya hannu a madadin Najeriya, yayin da Dakta Khaleed H. Al-Biyari ya sanya hannu a madadin Gwamnatin Masarautar Saudiyya.

Ministar ya bayyana cewa, wannan ci gaban babbar dama ce da za ta ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu da kuma taimakawa wajen fuskantar ƙalubalen tsaro da Najeriya ke fuskanta a halin yanzu.

Ya ce, ma’aikatar tsaron Najeriya tana maraba da wannan ci gaba, tare da fatan hakan zai taimaka wajen kawo ƙarshen matsalolin tsaro da ake fama da su a sassa daban-daban na ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa