Layin Dogo Na Habasha-Djibouti Na Habaka Kasuwanci Da Karfafa Hada-hadar Kayayyaki
Published: 17th, March 2025 GMT
Wasu manyan jami’an kasar Habasha sun bayyana cewa, layin dogon da ya sada tsakanin kasar Habasha da Djibouti da kasar Sin ta gina, yana kara inganta bangaren hada-hadar kayayyaki na kasar Habasha, kana ya zama wani muhimmin ginshiki da ke taimaka wa cinikayyar shigo da kaya da fitar da su zuwa kasashen waje a kasar.
Jami’an sun bayyana hakan ne a wata ganawa da suka yi tare da masu ruwa da tsaki a harkar sufuri da shigo da kayayyaki da fitar da su waje na kasar Habasha, a ranar Asabar da ta gabata.
Da yake jawabi a wajen taron, ministan sufuri da hada-hadar kayayyaki na kasar Habasha, Alemu Sime ya bayyana cewa, kasar da ke gabashin Afirka tana aiki tukuru don zamanantar da fannin sufuri da hada-hadar kayayyaki, a wani bangare na burin da ta sa a gaba wajen kawo sauyi ga harkokin cinikayyar shigo da kayayyaki da fitar da su waje.
Ya ce, layin dogo da ya sada tsakanin kasar Habasha da Djibouti mai tsawon kilomita 752, yana kara kaimin tabbatar da cikar burin kasar, yana mai bayyana muhimmancin ingantawa da fadada samar da harkokin sufurin ababen hawa da kayayyaki, tare da mayar da hankali musamman a kan layukan dogo. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: hadar kayayyaki kasar Habasha
এছাড়াও পড়ুন:
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
A cewarsa, damar kauwancin da ake samu daga fannin an same ta ne, saboda yadda Matatar ta Dangote, ke sarrafa danyen Mai wanda kuma ‘ya’yan kungiyar, ke son ganin sun amafana da hakan daga Matatar ta Dangote.
Madugu ya ci gaba da cewa, wasu daga cikin bangarorin da kungiyar za ta amfana daga Matatar ya ce, sun hada da, Man da ake sarrafawa daga danye Mai, Man Dizil, Kalanzir, Man Jirgin Sama da kuma Iskar Gas, samfarin LPG.
Sauran ya ce, sun ne, sanadaran naphtha, bitumen, ethylene, propylene da sauransu.
Kazalika, ya kuma jinjinawa Shugaban rukunin Matatar Man ta Dangote, Aliko Dangote, bisa namijin kokarin da ya yi, na kafa Matatar Man a kasar nan.
Tawagar ta kungiyar MAN, ta kuma karrama Dangote da mai bai wa shugaban kasa shawara ta musamman a bangaren hudda da jama’a da kuma jagorar aikin rukunin Matatar Madam Fatima Wali-Abdurrahman da babbar lambar yabo.
A kwanan baya ne, Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya amince da sanya kaso 15 a cikin dari kan Man Fetur da Man Dizil da ake shigowa da su cikin kasar daga ketare, inda danganta tsarin, a matsayin matakin sarrafa Mai a cikin kasar da kuma rage yin dogaro kan makamashin da ake shigowa da shi, daga waje.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA