Wasu manyan jami’an kasar Habasha sun bayyana cewa, layin dogon da ya sada tsakanin kasar Habasha da Djibouti da kasar Sin ta gina, yana kara inganta bangaren hada-hadar kayayyaki na kasar Habasha, kana ya zama wani muhimmin ginshiki da ke taimaka wa cinikayyar shigo da kaya da fitar da su zuwa kasashen waje a kasar.

Jami’an sun bayyana hakan ne a wata ganawa da suka yi tare da masu ruwa da tsaki a harkar sufuri da shigo da kayayyaki da fitar da su waje na kasar Habasha, a ranar Asabar da ta gabata.

Da yake jawabi a wajen taron, ministan sufuri da hada-hadar kayayyaki na kasar Habasha, Alemu Sime ya bayyana cewa, kasar da ke gabashin Afirka tana aiki tukuru don zamanantar da fannin sufuri da hada-hadar kayayyaki, a wani bangare na burin da ta sa a gaba wajen kawo sauyi ga harkokin cinikayyar shigo da kayayyaki da fitar da su waje.

Ya ce, layin dogo da ya sada tsakanin kasar Habasha da Djibouti mai tsawon kilomita 752, yana kara kaimin tabbatar da cikar burin kasar, yana mai bayyana muhimmancin ingantawa da fadada samar da harkokin sufurin ababen hawa da kayayyaki, tare da mayar da hankali musamman a kan layukan dogo. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hadar kayayyaki kasar Habasha

এছাড়াও পড়ুন:

Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana

shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibof ya bayyana cewa asarorin da HKI ta yi a yakin kwanaki 12 da JMI suna da yawa. Kuma babu shakka ya fi abinda ta bayyana.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban majalisar dokokin kasar ta Iran yana fadar haka a lokacinda yake hira da wata tashar talabijin a nan Tehran . Ya kuma kara da cewa. Maganar cewa uahudawa 3500 kawai suka ji rauni a yakim gaba daya karya ce.

Qalibof ya ce yana da tabbacin cewa yahudawa akalla 500 suna halaka sanadiyyar hare-haren da sojojin Iran suka kai a kan HKI a yankin kwamaki 12. .

Ya ce sojojin yahudawan sun saba boye yawan mutanen da suka halaka a yake-yaken da take fafatawa da masu gwagwarmaya a yankin. suna kuma hana yada hutunan bidyo na asarorin da suka yi a yaki. masili daga cikin wasu da dama shi ne yadda suka hada yar rahoton tashar talabijin ta Aljazeera daukar hotuna a yakin saboda basa son muatane su san gaskiya. su kuma ga irin yawan asarorin da suka yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a sa zare tsakanin Amurka da Turai kan harajin kasuwanci
  • Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika
  • Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani
  • An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
  • Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana
  • Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari