Cibiyar Bincike Kan Harkar Noma (IAR) tare da hadin gwiwar Hukumar Yada Sakamakon Bincike da Wayar da Kan Manoma ta Kasa (NAERLS), Jami’ar Ahmadu Bello Zaria, sun shirya taron kwana guda a Kaduna domin masu ruwa da tsaki kan aikin bunkasa noman dawa a Najeriya.

 

Taken taron shi ne: “Gabatarwa da Tattaunawa Kan Amfanin Sabbin Nau’ikan Dawa Masu Jure Sauyin Yanayi Domin Rage Talauci da Inganta Abinci a Najeriya.

 

Daga cikin manyan abokan aikin akwai Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS), Kungiyar Manoman Dawa da Masara ta Najeriya, da Tarayyar Turai (EU), da sauransu.

A jawabin sa, Mataimakin Daraktan NAERLS, Farfesa Muhammad Musa Jaliya, ya ce babban burin taron shi ne tabbatar da dorewar sabon tsarin nomar dawa a Najeriya.

 

“Ba ma so mu gudanar da aikin kawai ya ƙare ba tare da dorewa ba. Babban dalilin wannan taro shi ne samar da mafita don dorewar aikin. Manoma sun rungumi aikin, kuma sun samu sauyi ta fuskar iri na dawa masu inganci da fa’ida,” in ji shi.

 

A tattauna da Radio Nigeria Kaduna, Shugaban Kungiyar Manoman Dawa ta Kasa, Dr. Adamu Yusuf, ya jaddada muhimmancin Najeriya a matsayin jagora a noman dawa a duniya. Ya ce ya kamata ‘yan Najeriya su ci gaba da addu’a da kokari domin kasar ta ci gaba da rike matsayinta a matsayin kasa ta daya ko ta biyu wajen noman dawa a duniya.

 

Ita ma a nata jawabin, Farfesa Aisha AbdulKadir daga IAR, ABU Zaria, ta bayyana cewa sun samu nasarar gabatar da sabbin nau’ikan iri na dawa a Najeriya.

 

“Muna son ganin mutane sun rungumi wadannan nau’ikan iri, muna kuma neman jin ra’ayoyin masu ruwa da tsaki da manoma don mu kara samun ci gaba,” in ji ta.

 

Wakilin ECOWAS a taron, Farfesa Mamman Saleh, ya bayyana cewa ECOWAS ta kuduri aniyar inganta rayuwar al’ummomin yankin ta hanyar bunkasa tattalin arziki da ayyukan noma.

“ECOWAS ta kafa hukumar kula da harkokin noma da albarkatun kasa domin tallafa wa ayyukan noman dawa na musamman, da nufin samar da ayyukan yi ga matasa da inganta gina kasa, da kuma dawo da filayen noma da suka lalace,” in ji shi.

 

Masu halarta taron sun fito ne daga Jihar Kaduna da sassa daban-daban da ke da alaka da harkar noman dawa.

 

Cov/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Dawa Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Ministocin Harkokin Wajen Iran da na Rasha sun Tattauna  Gabanin Taron Kwamitin Gwamnonin IAEA

Ministocin harkokin wajen Iran da na Rasha sun tattauna ta  wayar tarho gabanin taron kwamitin gwamnonin IAEA

A yayin tattaunawar Araghchi da Lavrov, sun yi musayar ra’ayi kan batutuwa daban-daban, ciki har da rikicin kan iyaka tsakanin Pakistan da Afghanistan, tare da jaddada muhimmancin yin shawarwari don warware batutuwan da ba su dace ba.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya kuma jaddada bukatar tuntubar juna tsakanin Iran da Rasha da ma sauran kasashen duniya domin lalubo hanyoyin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A yayin da yake ishara da matakin da Amurka da kawayenta na Turai suka dauka a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya dangane da Falasdinu, da wani daftarin kuduri na kafa rundunar kasa da kasa a Gaza, Araghchi ya ce irin wannan shiri ba zai yi nasara ba saboda ya saba wa ka’idojin ‘yanci da hakkin al’ummar Palasdinu na cin gashin kansu.

Lavrov ya bayyana aniyar Moscow na ci gaba da tuntubar juna tsakanin kasashen biyu da na shiyya-shiyya, da nufin tabbatar da tsaro ta hanyar hadin gwiwa da juna.

Bangarorin biyu sun kuma yi musayar ra’ayi kan hadin gwiwar Iran da hukumar ta IAEA, inda suka jaddada wajabcin ci gaba da tuntubar juna da yin aiki tare tsakanin Tehran, Moscow, da Beijing a wannan fanni.

Wannan ya biyo bayan ganawar da wakilan kasashen Sin da Iran da kuma Rasha suka yi ne da babban daraktan hukumar Rafael Grossi da tawagarsa a taron kwamitin gwamnonin na IAEA mai zuwa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iraki: Hukumar Zabe Ta Fara Sanar Da Sakamakon Farko Na Babban Zaben Da Aka Gudanar November 13, 2025 Kenya: An gano tarin zinari a karkashin kasa da darajarsa ta haura Dala biliyan 5 November 13, 2025 Gaza: Hamas Ta Nemi Kawo Karshen Kisan Kiyashi Da Lamunce  Shigar Da Taimako November 13, 2025 MDD ta yi gargadi game da hadarin yunwa a wasu sassa na duniya November 13, 2025 Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza November 12, 2025 Shugaban Iran Ya Aike Da Wasika Ta Musamman Zuwa Ga Yarima Mai Jiran Gado Na Saudiyya November 12, 2025 Gwamntin Nijeriya tace Za ta Kare Sojojinta Da Ke Bakin Aiki November 12, 2025 Iran Da Pakistan Sun yi Kira Da Yin Aiki Tare Don Tunkarar  Makiyansu November 12, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Kan Rikicin Yankin November 12, 2025 Gabon: An Daure Mata Da ‘Dan  Tsohon Shugaban Kasa Bongo Shekaru 20 A Gidan Yari November 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da ya kamata PDP ta jingine taron da za ta gudanar— Saraki
  • NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
  • Ministocin Harkokin Wajen Iran da na Rasha sun Tattauna  Gabanin Taron Kwamitin Gwamnonin IAEA
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Ka’idoji Ga Samar da Injinan Noma a Najeriya
  • PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu
  • CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15
  • Kotu ta sake dakatar da babban taron PDP
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU