IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
Published: 21st, March 2025 GMT
Cibiyar Bincike Kan Harkar Noma (IAR) tare da hadin gwiwar Hukumar Yada Sakamakon Bincike da Wayar da Kan Manoma ta Kasa (NAERLS), Jami’ar Ahmadu Bello Zaria, sun shirya taron kwana guda a Kaduna domin masu ruwa da tsaki kan aikin bunkasa noman dawa a Najeriya.
Taken taron shi ne: “Gabatarwa da Tattaunawa Kan Amfanin Sabbin Nau’ikan Dawa Masu Jure Sauyin Yanayi Domin Rage Talauci da Inganta Abinci a Najeriya.
Daga cikin manyan abokan aikin akwai Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS), Kungiyar Manoman Dawa da Masara ta Najeriya, da Tarayyar Turai (EU), da sauransu.
A jawabin sa, Mataimakin Daraktan NAERLS, Farfesa Muhammad Musa Jaliya, ya ce babban burin taron shi ne tabbatar da dorewar sabon tsarin nomar dawa a Najeriya.
“Ba ma so mu gudanar da aikin kawai ya ƙare ba tare da dorewa ba. Babban dalilin wannan taro shi ne samar da mafita don dorewar aikin. Manoma sun rungumi aikin, kuma sun samu sauyi ta fuskar iri na dawa masu inganci da fa’ida,” in ji shi.
A tattauna da Radio Nigeria Kaduna, Shugaban Kungiyar Manoman Dawa ta Kasa, Dr. Adamu Yusuf, ya jaddada muhimmancin Najeriya a matsayin jagora a noman dawa a duniya. Ya ce ya kamata ‘yan Najeriya su ci gaba da addu’a da kokari domin kasar ta ci gaba da rike matsayinta a matsayin kasa ta daya ko ta biyu wajen noman dawa a duniya.
Ita ma a nata jawabin, Farfesa Aisha AbdulKadir daga IAR, ABU Zaria, ta bayyana cewa sun samu nasarar gabatar da sabbin nau’ikan iri na dawa a Najeriya.
“Muna son ganin mutane sun rungumi wadannan nau’ikan iri, muna kuma neman jin ra’ayoyin masu ruwa da tsaki da manoma don mu kara samun ci gaba,” in ji ta.
Wakilin ECOWAS a taron, Farfesa Mamman Saleh, ya bayyana cewa ECOWAS ta kuduri aniyar inganta rayuwar al’ummomin yankin ta hanyar bunkasa tattalin arziki da ayyukan noma.
“ECOWAS ta kafa hukumar kula da harkokin noma da albarkatun kasa domin tallafa wa ayyukan noman dawa na musamman, da nufin samar da ayyukan yi ga matasa da inganta gina kasa, da kuma dawo da filayen noma da suka lalace,” in ji shi.
Masu halarta taron sun fito ne daga Jihar Kaduna da sassa daban-daban da ke da alaka da harkar noman dawa.
Cov/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya sheƙar da ’yan siyasa daga ɓangarori daban-daban suke yi.
A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa Jam’iyyar APC mai mulki ta jawo ɗiga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaɓen 2027.
Hakan dai yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu ’yan ƙasar suke kokawa bisa yadda ake gudanar da mulki da kuma yadda wasu manyan ’yan siyasa suke fadi-tashin kafa wata inuwa da suka ce za ta ciro wa talaka kitse a wuta ta hanyar kawar da gwamnatin APC.
NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaWannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai da nufin gano alƙiblar da siyasar Najeriya take shirin fuskanta.
Domin sauke shirin. Latsa nan