Aminiya:
2025-04-30@22:52:30 GMT

Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno

Published: 1st, March 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Mandalari da ke Konduga a Jihar Borno, ta hallaka mutane biyu tare da jikkata wasu da dama.

Gobarar, ta tashi da misalin ƙarfe 11:25 na safiyar Juma’a, 28 ga watan Fabrairu, 2025, ta bazu zuwa yankunan da ke da cunkoson jama’a, inda ta cinye matsugunan wucin gadi da kuma kayayyaki masu tarin yawa.

Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Sojojin da aka jibge a Konduga, sun kai ɗauki nan take bayan samun labarin tashin wutar.

Sun haɗa kai da jami’an agaji da kuma al’ummar yankin domin shawo kan gobarar.

Duk da haka, akwai fargabar cewa yawan mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.

Dakarun Operation Haɗin Kai da ke aiki a Konduga sun taka rawar gani wajen ceto mutane da kuma hana gobarar bazuwa.

“Sojoji sun kawo ɗauki cikin gaggawa, tare da tattara ma’aikata da kayan aiki don shawo kan gobarar da kare mutanen da lamarin ya shafa,” in ji wata majiya daga jami’an tsaro.

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno, tare da haɗin gwiwar sojoji da hukumomin agaji, na ci gaba da ƙoƙarin shawo kan lamarin.

Hakazalika, an tura ƙungiyoyin lafiya domin kula da waɗanda suka jikkata.

Wannan ba shi ne karon farko da sansanin Mandalari ke fuskantar irin wannan iftila’i ba.

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, tsakanin watan Fabrairu da Yunin shekarar 2024, gobara ta tashi aƙalla sau 43 a sansanin, lamarin da ya haddasa asarar rayuka da dukiyoyi masu tarin yawa.

Shugaban al’ummar yankin, Bulama, ya yaba da ƙoƙarin jami’an tsaro a Konduga, inda ya ce suna bayar da muhimmiyar gudunmawa ba kawai wajen magance rikice-rikice ba, har ma da tabbatar da tsaron ’yan gudun hijira.

“Muna godiya ga taimakon Allah SWT da nasu, domin ba don agajin sojoji ba, da lamarin zai iya yin muni matuƙa,” in ji shi.

A halin yanzu, hukumomi sun buƙaci ’yan gudun hijira da su ƙara yin taka-tsantsan domin hana sake faruwar irin wannan gobara, musamman a wannan lokaci na zafi.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), na ci gaba da rabon kayan tallafi, yayin da hukumomin tsaro suka tabbatar da cewa za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Sansanin yan gudun hijira yan gudun hijira

এছাড়াও পড়ুন:

Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya yaba da ziyarar da cibiyar ta kai Zamfara domin duba ƙoƙarin gwamnati na magance matsalar rashin tsaro a jihar.

 

“Ina yawan cewa, idan ku ka yi ƙoƙarin shawo kan Zamfara yadda ya kamata ta fuskar rashin tsaro, za ku magance kashi 80 na matsalolin tsaro a Arewa.

 

“Daga dukkan tsare-tsaren da na gani ya zuwa yanzu, mun mallaki abin da ake buƙata domin tunkarar waɗannan ƙalubale bisa tuntubar juna da haxin gwiwa tsakanin jihar Zamfara da ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, wannan abin a yaba ne.

 

“Na yi farin ciki da jin cewa Tarayyar Turai ta ware wasu kuɗaɗe, duk da cewa za mu samar da wani asusu, a Zamfara a shirye muke mu ba da tallafin, idan kun shirya gobe, mu ma mun shirya.

 

“Mun shirya, kuma ƙofar mu a buɗe take, duk wani abu da zai kawo sauyi mai kyau a Zamfara muna maraba da shi, muna buƙatar tsari na abin da ku ke yi domin mu ci gaba da bin diddigin lamarin, zan samu wata tawaga da za ta riƙa hulɗa da cibiyar yaƙi da ta’addanci.

 

Tun da farko, Shugabar Rigakafi da Yaƙi da Ta’addanci (PCVE), Ambasada Mairo Musa Abbas ta ce, tawagar ta zo jihar Zamfara ne a madadin mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu da kuma kodinetan yaƙi da ta’addanci na ƙasa, Manjo Janar Adamu Garba Laka. “Muna nan a matsayin wani bangare na dabarun bayar da shawarwari na ƙasa baki ɗaya.”

 

“Muna son sake gode muku bisa irin karramawar da ka yi mana a Jihar Zamfara da kuma irin shugabancin da ka yi wa al’umma, muna sa ran haɗin kai don ganin cewa Zamfara ta zama kan gaba wajen yaƙi da ‘yan bindiga.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara