Aminiya:
2025-06-15@07:47:19 GMT

Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno

Published: 1st, March 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Mandalari da ke Konduga a Jihar Borno, ta hallaka mutane biyu tare da jikkata wasu da dama.

Gobarar, ta tashi da misalin ƙarfe 11:25 na safiyar Juma’a, 28 ga watan Fabrairu, 2025, ta bazu zuwa yankunan da ke da cunkoson jama’a, inda ta cinye matsugunan wucin gadi da kuma kayayyaki masu tarin yawa.

Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Sojojin da aka jibge a Konduga, sun kai ɗauki nan take bayan samun labarin tashin wutar.

Sun haɗa kai da jami’an agaji da kuma al’ummar yankin domin shawo kan gobarar.

Duk da haka, akwai fargabar cewa yawan mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.

Dakarun Operation Haɗin Kai da ke aiki a Konduga sun taka rawar gani wajen ceto mutane da kuma hana gobarar bazuwa.

“Sojoji sun kawo ɗauki cikin gaggawa, tare da tattara ma’aikata da kayan aiki don shawo kan gobarar da kare mutanen da lamarin ya shafa,” in ji wata majiya daga jami’an tsaro.

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno, tare da haɗin gwiwar sojoji da hukumomin agaji, na ci gaba da ƙoƙarin shawo kan lamarin.

Hakazalika, an tura ƙungiyoyin lafiya domin kula da waɗanda suka jikkata.

Wannan ba shi ne karon farko da sansanin Mandalari ke fuskantar irin wannan iftila’i ba.

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, tsakanin watan Fabrairu da Yunin shekarar 2024, gobara ta tashi aƙalla sau 43 a sansanin, lamarin da ya haddasa asarar rayuka da dukiyoyi masu tarin yawa.

Shugaban al’ummar yankin, Bulama, ya yaba da ƙoƙarin jami’an tsaro a Konduga, inda ya ce suna bayar da muhimmiyar gudunmawa ba kawai wajen magance rikice-rikice ba, har ma da tabbatar da tsaron ’yan gudun hijira.

“Muna godiya ga taimakon Allah SWT da nasu, domin ba don agajin sojoji ba, da lamarin zai iya yin muni matuƙa,” in ji shi.

A halin yanzu, hukumomi sun buƙaci ’yan gudun hijira da su ƙara yin taka-tsantsan domin hana sake faruwar irin wannan gobara, musamman a wannan lokaci na zafi.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), na ci gaba da rabon kayan tallafi, yayin da hukumomin tsaro suka tabbatar da cewa za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Sansanin yan gudun hijira yan gudun hijira

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump ya umarci jami’an hukumar kula da shige-da-ficen-kasar da su dakatar da aikin samamen kama baƙin-haure ’yan ci-rani, a gonaki da otal-otal da ma gidajen sayar da abinci na fadin kasar.

Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito ma’aikatar tsaron cikin gida na tabbatar da samun umarnin, wanda aka mika shi ga hukumar kula da shige-da-fice da kuma ta yaki da fasa-kwauri, to sai dai kamfanin dillancin labarai na Reuters bai kai ga tabbatar da sahihancin umarnin ba.

’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe

Tun a lokacin yakin neman zaben shugabancin Amurka zango na biyu ,Mista Trump ya alkawarta korar bakin-hauren da suka shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

To sai dai wannan mataki ya fuskanci kakkausan suka sakamakon yadda ake kame mutanen da ba su taba aikata laifin komai ba, musamman wadanda ke aiki a gonaki da sauran wurare, lamarin da ya janyo barkewar zanga-zanga a wasu sassan kasar.

Rahotanni sun tabbatar da cewa kawo yanzu an shafe kwanaki ana tarzoma a birnin Los Angeles na Jihar California ta Amurka, inda masu zanga-zanga ke dauki-ba-dadi da dakarun tsaron kasa da Shugaba Trump ya tura tun farko domin kwantar da zanga-zangar da ta barke sakamakon kamen bakin haure.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122