Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno
Published: 1st, March 2025 GMT
Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Mandalari da ke Konduga a Jihar Borno, ta hallaka mutane biyu tare da jikkata wasu da dama.
Gobarar, ta tashi da misalin ƙarfe 11:25 na safiyar Juma’a, 28 ga watan Fabrairu, 2025, ta bazu zuwa yankunan da ke da cunkoson jama’a, inda ta cinye matsugunan wucin gadi da kuma kayayyaki masu tarin yawa.
Sojojin da aka jibge a Konduga, sun kai ɗauki nan take bayan samun labarin tashin wutar.
Sun haɗa kai da jami’an agaji da kuma al’ummar yankin domin shawo kan gobarar.
Duk da haka, akwai fargabar cewa yawan mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.
Dakarun Operation Haɗin Kai da ke aiki a Konduga sun taka rawar gani wajen ceto mutane da kuma hana gobarar bazuwa.
“Sojoji sun kawo ɗauki cikin gaggawa, tare da tattara ma’aikata da kayan aiki don shawo kan gobarar da kare mutanen da lamarin ya shafa,” in ji wata majiya daga jami’an tsaro.
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno, tare da haɗin gwiwar sojoji da hukumomin agaji, na ci gaba da ƙoƙarin shawo kan lamarin.
Hakazalika, an tura ƙungiyoyin lafiya domin kula da waɗanda suka jikkata.
Wannan ba shi ne karon farko da sansanin Mandalari ke fuskantar irin wannan iftila’i ba.
Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, tsakanin watan Fabrairu da Yunin shekarar 2024, gobara ta tashi aƙalla sau 43 a sansanin, lamarin da ya haddasa asarar rayuka da dukiyoyi masu tarin yawa.
Shugaban al’ummar yankin, Bulama, ya yaba da ƙoƙarin jami’an tsaro a Konduga, inda ya ce suna bayar da muhimmiyar gudunmawa ba kawai wajen magance rikice-rikice ba, har ma da tabbatar da tsaron ’yan gudun hijira.
“Muna godiya ga taimakon Allah SWT da nasu, domin ba don agajin sojoji ba, da lamarin zai iya yin muni matuƙa,” in ji shi.
A halin yanzu, hukumomi sun buƙaci ’yan gudun hijira da su ƙara yin taka-tsantsan domin hana sake faruwar irin wannan gobara, musamman a wannan lokaci na zafi.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), na ci gaba da rabon kayan tallafi, yayin da hukumomin tsaro suka tabbatar da cewa za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Sansanin yan gudun hijira yan gudun hijira
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
Sama da mutum 100 daga cikin jami’an tsaron al’umma da Gwamnatin Katsina ta samar ne suka suka mutu a yayin aikin karaɗe ’yan bindiga da suka addabi al’ummomin jihar.
Wannan ƙari ne a kan sojoji da kuma aƙalla jami’an ’yan sanda 30 da suka rasu a yayin aikin tabbatar da tsaron rayuwa da duniyoyin al’umma, a cewar ma’aikatar tsaron jihar.
Kwamishinan tsaron jihar, Nasir Mua’zu ya sanar da haka ne a martaninsa kan wasu rahotanni da ke yawo a kafofin sada zumunta, waɗanda ya ce ana amfani da su domin tayar da hankalin jama’a.
Mu’azu ya ce Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Raɗɗa yana yin iya bakin koƙarinsa wajen shawo kan matsalar ’yan ta’adda kuma ana samun nasara a kansu.
Kwamishinan ya ce lokacin da Gwamna Raɗɗa ya karbi shugabancin Jihar Katsina, ƙananan hukumomi aƙalla 24 ne ke fama da matsalar ’yan bindiga, amma kuma sakamakon haɗin kai da jami’an tsaro da kuma ƙirƙiro ƙungiyar ’yan sa-kai ta jihar, an yi nasarar murƙushe su a ƙananan hukumomi 11.
Mu’azu ya ce, matsalar ta kuma yi sauƙi a wasu ƙananan hukumomi tara, in banda Faskari da Ƙankara da Safana da kuma Matazu, da ke ci gaba da dama da hare-hare.
Ya bayyana cewa hakan ba ya nufin cewa gwamnati ta gaza, domin jami’an tsaro na iya bakin ƙoƙarinsu wajen tabbatar da tsaron lafiya da duniyoyin al’umma a wuraren.
A cewarsa, duk da hatsarin da gwamnan ya yi kwanakin baya, bai daina tattaunawa da shugabannin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a harkar tsaro ba da ke jihar, domin shawo kan matsalar.
Don haka ya buƙaci haɗin kai daga kowanne ɓangare, musamman ganin yadda jami’an tsaron ke sadaukar da rayukansu wajen kare lafiya.