Aminiya:
2025-04-30@19:31:46 GMT

Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250

Published: 1st, March 2025 GMT

Ofishin Jakadancin Saudiyya da ke Jihar Kano, ya bai wa jihar da wasu jihohin Arewa kyautar dabino katan 1,250, a matsayin wani ɓangare na shirin tallafin Ramadan na kowace shekara.

Wannan shiri na cikin ayyukan jin-ƙai da Cibiyar Sarki Salman (KSrelief), ke gudanarwa don tallafa wa masu buƙata da kuma ƙarfafa dangantakar Saudiyya da Najeriya.

Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn

Yayin bikin rabon dabinon, Jakadan Saudiyya a Kano, Khalil Admawy, ya gode wa Sarki Salman bin Abdulaziz da Yarima Mai jiran gado Mohammed bin Salman bisa ƙoƙarinsu na ci gaba da tallafa wa al’ummar Musulmi a faɗin duniya.

Ya jaddada aniyar Saudiyya na ci gaba da taimaka wa Musulmai, musamman a lokacin watan Ramadan.

A bana, Saudiyya ta ware tan 50 na dabino don raba wa a Kano da wasu jihohin Arewa, baya ga tan 60 da aka riga aka aike Abuja a makon da ya gabata.

Ana ci gaba da shirin rabawa don tabbatar da cewa dukkanin kayan sun isa hannun buƙata.

Jakadan Saudiyya, ya kuma bayyana cewa shirin buɗa baki na ƙasar zai fara aiki ne a Abuja a ranar 3 ga watan Ramadan, inda za a raba wa Musulmai masu azumi abinci kyauta.

Ya kuma yi bayani kan irin ayyukan jin-ƙai da Cibiyar Sarkin ke yi a duniya, inda ya ce tuni cibiyar ta kammala sama da ayyuka 2,500 da darajarsu ta haura dala biliyan bakwai, waɗanda suka amfanar da ƙasashe 91.

A nasa ɓangaren, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Umar Farouk, ya wakilta, ya nuna godiyarsa ga wannan kyauta.

Ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Kano za ta tabbatar da cewa an raba dabinon ga waɗanda suka dace su amfana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa kyauta Ramadan Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano

CP Bakori ya gode wa al’ummar Kano saboda goyon bayan da suke ba su a ƙoƙarin su na yaƙar masu aikata laifuka tare da kira ga ci gaba da haɗin kai wajen kai rahoton abubuwan da suke zargi ga Ƴansanda.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano