Aminiya:
2025-07-10@23:45:23 GMT

Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine

Published: 17th, March 2025 GMT

Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce yana shirin tuntuɓar takwaransa na Rasha Vladimir Putin da zummar tattauna batun kawo ƙarshen yaƙin Ukraine.

Trump ya shaida wa manema labarai hakan a cikin jirgin shugaban ƙasa na Airforce One a kan hanyarsa ta zuwa Washington daga Florida cewa yana ƙoƙarin ganin cewa yaƙin ya zo ƙarshe.

Madalla da hutu ga ’yan makaranta domin azumi Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala

Trump ya bayyana cewa an yi aiki sosai a game da kawo ƙarshen wannan rikici a cikin ƙarshen makon da ya gabata.

Trump na ƙoƙarin samun goyon bayan Putin a game da tayin tsagaita wuta na kwanaki 30, wanda Ukraine ta aminnce da shi a makon jiya.

Sai dai ana ci gaba da miƙa tayin ne a yayin da dukkannin ɓangarorin ke ci gaba da yi wa juna luguden wuta ta sama, har sai da sojin Rasha suka kusan fatattakar dakarun Ukraine a yankin Kursk.

A ranar Juma’a, Fadar Gwamnatin Rasha, Kremlin ta ce shugaba Putin ya aike da saƙo zuwa ga Trump a game da tsagaita wuta ta hannun manzon Amurka na musamman, Steve Witkoff, wanda ya ziyarci Moscow, inda yake bayyana aniyar tsagaita wuta amma da taka-tsantsan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Tabbatar Da Cewa Tana Iya Yakar Amurka Da HKI A Lokaci Guda

Tsohon babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci wato IRGC ya bayyana cewa a yakin da JMI ta fafata a cikin watan da ya gabata , ya tabbata cewa JMI tana iya yaki da Amurka da HKI a lokaci guda.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Manjo Janar Mohsen Rezaei, yana fadar haka a lokacinda wata talabijin ta cikin gida take hira da shi a jiya Talata .

Labarin ya kara da cewa Janar Rezaei ya taba rike mukamin babban kwamandar rundunar IRGC jim kadan bayan nasarar juyin juya halin musulunci a shekara 1979.

Yace: Shahid Janar Qasem Sulaimani, Babban kwamandan rundunar Qudus ne  ya fara furta zancen cewa , Iran tana da karfin fuskantar Amurka. Wannan kuma ya tabbata a yankin kwanaki 12 da aka dorawa kasar.

A halin yanzu dai Janar Rezaei yana cikin wadanda suke bawa Jagoran juyin juya halin musulunci shawara a kan al’amuran tsaro da siyasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki
  • An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya
  • Iran Ta Musanta Neman Ci Gaba Da Gudanar Da Tattaunawa Da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Iran Ta Tabbatar Da Cewa Tana Iya Yakar Amurka Da HKI A Lokaci Guda
  • Amurka Tana Fatan HKI da Hamas Su Tsaida Budewa Juna Wuta Na Kwanaki 60 A Karshen Wannan makon
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi