Aminiya:
2025-05-01@03:54:27 GMT

Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza

Published: 18th, March 2025 GMT

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta inda ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasɗinawa a Zirin Gaza.

Sabbin hare-haren da Isra’ila ta ƙaddamar sun kashe fiye da mutum 200 ciki har da mata da yara tare da jikkata daruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti.

Mahaifina ne kaɗai shugaban da bai damu ya azurta kansa ba — Seyi Tinubu Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano

Hamas ta ce Isra’ila ta kai harin na ba-zata ne kan fararen hula da ta shammata a ƙoƙarin ta na keta yarjejeniyar tsagaita wutar da suka ƙulla tun a ranar 19 ga watan Janairu.

Kazalika, dakarun tsaron Isra’ila (IDF) sun ce sun kai hari kan abin da suka kira wuri mai ‘barazanar ta’addanci’ na Hamas.

Wannan dai shi ne hari mafi girma da aka kai a Gaza tun bayan da aka fara tsagaita wuta a ranar 19 ga watan Janairu yayin da aka gaza cimma matsaya a tattaunawar tsawaita wa’adin tsagaita wutar na Gaza..

Bayanai sun ce galibin waɗanda hare-haren suka rutsa da su mutane da ke cin abincinsu na Sahur kafin fitowar alfijir.

Majiyoyi sun ce sama da jiragen yaƙin Isra’ila 20 ne suka yi shawagi a sararin sama, sannan suka soma luguden wuta a garuruwan Gaza da Rafah da Khan Younis.

Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da Ministan Tsaro Isra’ila Katz ne suka ba da umarnin kai hare-haren a safiyar ranar Talata, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin Firayim Minista ta sanar.

BBC ya ruwaito cewa an kashe Mahmoud Abu Wafah, mataimakin ministan harkokin cikin gida a Gaza kuma babban jami’in tsaron Hamas a yankin.

Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta ce kawo yanzu aƙalla Falasɗinawa 48,572 ne aka tabbatar da mutuwarsu yayin da wasu 112,032 suka jikkata a yakin da Isra’ila ke yi a Gaza.

Ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza ya sabunta alƙaluman waɗanda suka mutu zuwa fiye da 61,700, yana mai cewa dubban Falasɗinawa da suka bace a ƙarƙashin baraguzan ginin ana kyautata zaton sun mutu.

Aƙalla mutane 1,139 ne aka kashe a Isra’ila a harin da Hamas ta jagoranta a ranar 7 ga Oktoba, 2023, sannan sama da 200 aka kama.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno

Wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya kashe aƙalla mutum 26, ciki har da mata da yara a kan hanyar Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a lokacin da motoci suka tayar da bama-baman da aka ɗana a gefen hanyar, da ya rutsa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida.

Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47 An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal

Majiyoyi, ciki har da wani babba soja, sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu da harin na baya bayan da safiyar ranar Talata.

Sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su suna kan hanyarsu ta tafiya Gamboru Ngala ne daga Rann lokacin da suka isa inda ‘yan ta’addan Boko Haram suka ɗana bam ɗin.

Bayanai sun ce baya ga mutum 26 da suka mutu, ƙarin mutum uku sun ji munanan raunuka.

“Mun tura wasu masu ba da agajin gaggawa inda lamarin ya auku domin kwashe mutane tare da tabbatar da tsaron sauran fararen-hula a wurin,” kamar yadda wata majiyar sojin da ba ta yarda a bayyana sunanta ba ta shaida wa Anadolu.

Ali Abass, wani ganau wanda ke tafiya a kan hanyar a lokacin da lamarin ya auku, ya ce sojojin da ‘yan sa-kai sun kai waɗanda suka jikkata wani asibiti. Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ‘yan’uwansa na cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Harin yana zuwa ne yayin da hare-hare ke ƙara ƙaruwa a yankin Tafkin Chadi, inda ‘yan ta’addan Boko Haram ke ƙara ƙaddamar da hare-haren bama-bamai da kwanton-ɓauna kan motocin fararen-hula da na sojoji.

An ba da rahoton hare-hare irin wannan a ranakun 21 ga watan Maris da 12 ga watan Afrilu. Kawo safiyar ranar Talata dai, jami’an tsaro a Borno ba su fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut