Aminiya:
2025-12-14@15:24:37 GMT

Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza

Published: 18th, March 2025 GMT

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta inda ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasɗinawa a Zirin Gaza.

Sabbin hare-haren da Isra’ila ta ƙaddamar sun kashe fiye da mutum 200 ciki har da mata da yara tare da jikkata daruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti.

Mahaifina ne kaɗai shugaban da bai damu ya azurta kansa ba — Seyi Tinubu Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano

Hamas ta ce Isra’ila ta kai harin na ba-zata ne kan fararen hula da ta shammata a ƙoƙarin ta na keta yarjejeniyar tsagaita wutar da suka ƙulla tun a ranar 19 ga watan Janairu.

Kazalika, dakarun tsaron Isra’ila (IDF) sun ce sun kai hari kan abin da suka kira wuri mai ‘barazanar ta’addanci’ na Hamas.

Wannan dai shi ne hari mafi girma da aka kai a Gaza tun bayan da aka fara tsagaita wuta a ranar 19 ga watan Janairu yayin da aka gaza cimma matsaya a tattaunawar tsawaita wa’adin tsagaita wutar na Gaza..

Bayanai sun ce galibin waɗanda hare-haren suka rutsa da su mutane da ke cin abincinsu na Sahur kafin fitowar alfijir.

Majiyoyi sun ce sama da jiragen yaƙin Isra’ila 20 ne suka yi shawagi a sararin sama, sannan suka soma luguden wuta a garuruwan Gaza da Rafah da Khan Younis.

Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da Ministan Tsaro Isra’ila Katz ne suka ba da umarnin kai hare-haren a safiyar ranar Talata, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin Firayim Minista ta sanar.

BBC ya ruwaito cewa an kashe Mahmoud Abu Wafah, mataimakin ministan harkokin cikin gida a Gaza kuma babban jami’in tsaron Hamas a yankin.

Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta ce kawo yanzu aƙalla Falasɗinawa 48,572 ne aka tabbatar da mutuwarsu yayin da wasu 112,032 suka jikkata a yakin da Isra’ila ke yi a Gaza.

Ofishin yada labarai na gwamnatin Gaza ya sabunta alƙaluman waɗanda suka mutu zuwa fiye da 61,700, yana mai cewa dubban Falasɗinawa da suka bace a ƙarƙashin baraguzan ginin ana kyautata zaton sun mutu.

Aƙalla mutane 1,139 ne aka kashe a Isra’ila a harin da Hamas ta jagoranta a ranar 7 ga Oktoba, 2023, sannan sama da 200 aka kama.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba

Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) ta bayyana cewa za ta gudanar da zanga-zangar ƙasa baki ɗaya a ranar 17 ga Disamba, 2025, domin nuna damuwarta kan taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya. Wannan sanarwa ta fito ne daga saƙon da NLC ta aikawa dukkanin majalisun jihohi a ranar 10 ga Disamba, bayan taron NEC da ta gudanar a ranar 4 ga watan. Kungiyar ta nuna baƙin ciki kan ƙaruwar hare-haren ƴan daba da satar mutane da ke ci gaba da addabar al’umma.

NLC ta mayar da hankali musamman kan sace ɗalibai mata a wata makarantar kwana da ke Jihar Kebbi a ranar 17 ga Nuwamba, inda ta bayyana mamaki cewa an janye jami’an tsaro daga makarantar kafin harin. Ta ce wannan lamari ne mummunan kuma abin takaici da ya kamata a bincike shi sosai tare da gurfanar da duk masu hannu a ciki. Ƙungiyar ta zargi gwamnati da gaza ɗaukar matakan da suka dace wajen kare rayukan ɗalibai a makarantu.

Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro Tinubu Na Ɗaukar Ƙwararan Matakai Don Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya – Shettima

Sanarwar ta ƙara da cewa an umarci dukkan rassan NLC da ƙungiyoyin ƙwadago da su “shirya cikakke” domin zanga-zangar. Ƙungiyar ta bayyana cewa yawaitar sace yara a makarantu ya kai wani mawuyacin matsayi da ba za a amince da shi ba. Ta jaddada cewa gwamnati na da nauyin kare makarantu, musamman waɗanda suke a karkara ko yankunan da ke fama da hare-hare.

ADVERTISEMENT

NLC ta ce dole ne gwamnati ta ɗauki mataki cikin gaggawa ta kammala bincike game da janye jami’an tsaro daga makarantar da aka kai harin, tare da ladabtar da masu laifi. A cewarta, rashin tsaron da ake fuskanta ya zama barazana ga rayuwa, da ilimi da ci gaban ƙasa. Saboda haka NEC ta umarci dukkan ƙungiyoyi da majalisun jihohi su fita ƙwansu da ƙwarƙwatarsu wajen zanga-zangar ranar 17 ga Disamba domin nuna rashin gamsuwarsu da yadda gwamnati ke tafiyar da batun tsaro.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP December 12, 2025 Manyan Labarai Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa December 12, 2025 Manyan Labarai Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su December 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan.
  • Farfesa Gumel Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Da Ke Dutse
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon  A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
  • MDD ta amince da wani kuduri da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza   
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta