Rwanda Ta Yanke Huladar Diflomasiyya Da Kasar Belgium
Published: 18th, March 2025 GMT
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Rwanda ya fitar, ta zargi kasar ta Belgium da tsoma baki a harkokin cikin gidanta.
Bugu da kari, sanarwar ta bai wa jakadan kasar Belgium a Kigali sa’o’i 48 da ya fice ya bar kasar.
Sanarwar ta kunshi cewa: A kodayaushe kasar Belgium tana kaskantar da Rwanda,tun kafin rikicin kasar DRC, da kuma bayansa, alhali kasar ta Belgium tana da dogon tarihi ta keta, musamman akan Rwanda.
Kasar Belgium dai ta dakatar da taimakon da take bai wa Rwanda saboda rawar da Kigali take takawa a rikicin kasar DRC.
A wani jawabi da shugaban kasar ta Rwanda ya yi a ranar Lahadi ya bayyana cewa; Kasarsa za ta kare manufofinta da hana kasashen waje yi ma ta katsalandan a harkokin cikin gidanta. Haka nan kuma ya zargi Belgium din da aikata laifuka a tsawon lokacin mulkin mallakar da ta yi wa kasarsa, yana mai kara da cewa za su ci gaba da fada da sabon salon mulkin mallaka.
Kasar ta Rwanda tana fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya saboda goyon bayan da take bai wa ‘yan tawayen kungiyar M23 da su ka kwace iko da manyan biranen Bukavu da Goma da suke a gabashin kasar DRC. Ana zargin cewa kasar ta Rwanda ta aike da sojoji 4000 da suke yaki a tare da ‘yan tawayen.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Belgium
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Wajabcin Kawo Karshen Ayyukan Ta’addanci A Kasashen Yanki
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Dole ne a kawar da ta’addanci ta hanyar hadin kan kasashen yanki
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin ta’addancin da aka kai a birnin Pahalgam na kasar Indiya, tare da nuna alhini da juyayinsa ga gwamnati da al’ummar kasar Indiya, yana mai jaddada bukatar hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin domin yakar ta’addanci da kuma tsayawa tsayin daka kan wannan barazana ta bai daya.
Pezeshkian ya zanta ta wayar tarho a yammacin jiya Asabar da fira ministan kasar Indiya Narendra Modi, inda suka tattauna kan sabbin al’amuran da suke faruwa a yankin na Indiya, da kuma alakar da ke tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kasar Indiya.