Iran An Dauke Wa Mahdi Karubi Daurin Talalar Da Aka Yi Masa A Gida
Published: 18th, March 2025 GMT
Dan Mahadi Karubi, wanda yana ya jagoranci boren 2009 bayan zaben shugaban kasa, ya bayyana cewa an daukewa mahaifin nashi daurin talalar da aka yi masa bisa umarnin ma’aikatar sharia.
Shi dai Mahadi Karubi an yi masa daurin zaman gidan ne bayan hargitsin da ya jagoranta bayan zaben shugaban kasar da aka yi a 2009.
Husain Karubi ya fada wa kamfanin dillancin labarun “IRNA” cewa; An fada wa mahaifina cewa, Daga nan zuwa watan Aprilu zai iya gudanar da rayuwarsa ta yau da kullum ba tare da kaidi ba, amma daga yanzu zuwa lokacin zai iya sanar da jami’an tsaro inda yake son zuwa gabanin kwana daya.
Harigitsin day a biyo bayan zaben 2009 a Iran wanda ‘yan takara uku fitattu su ka tsaya, da su ne Ahmadinejad da ya lashe zaben, sai kuma Mirhusain Musawi da Mahdi Karubi. Wadanda ba su ci zaben ba, sun riya cewa an yi magudi a zaben, lamarin da mahukunta su ka kure shi saboda rashin wani dalili da madogara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
Lamarin ya ci gaba da raguwa har zuwa 2024, inda yawan kudaden da ake kashewa a yawon ketare ya fadi da kaso 14 a matakin shekara-shekara zuwa dala biliyan 2.66.
Hakan na nuni da cewa ‘yan Nijeriya sun rage kashe kudaden da suke kashewa kan safarar jiragen sama da dala biliyan 1.12 ko kuma kashi 30 cikin dari a cikin shekaru biyun.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp