Aminiya:
2025-08-16@17:04:02 GMT

Tsofaffin furodusoshin Kannywood da aka daina jin ɗuriyarsu

Published: 18th, March 2025 GMT

Masana’antar Kannywood ta dade tana nishaɗantar da al’umma, musamman Hausawa da sauran kabilun Arewacin Najeriya.

A makon jiya Aminiya ta ruwaito a cewa kasuwancin fina-finan ya samu koma-baya matuƙa, wanda hakan ya sa wasu suke nuna yatsa ga furodusohin yanzu kan gaza shirya fim ɗin da za a iya haskawa a Netflix da sauran manyan hanyoyin nuna fina-finai da za su samar wa masana’antar kuɗin shiga.

NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza

Wannan ya sa Aminiya ta yi waiwayen wasu furodusohin da aka daina jin ɗuriyarsu a masana’antar.

Salisu Galadanchi – Shi ne Daraktan Fim din Turmin Danya, fim na farko a Kannywood, ya yi ritaya daga aikin gwamnati a Gidan Talabijin na CTV, yana zaune a Kano.

Umar Sheikh Mohammed: Shi ne mai Kamfanin Godiya and Dan Hassan wanda ya shirya fina-finan barkwanci, shi ma ya yi nukusani.

Bala Ahmed: Ana kiransa da Bala Sarauniya saboda rawar da ya taka wajen shiryawa da gabatar da finafinan Kamafanin Sarauniya Films a Kano.

Auwalu Mohammed Sabo shi ne Furodusan Kamfanin Sarauniya Films wanda suka yi finafinan gargajiya irin su Sangaya da Daskindaridi da Linzami da Wuta da sauransu. Yanzu yana aiki a Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Ali Jindos Aneesa: Tsohon mai daukar hoto na masana’antar, wanda ya koma shirya fim. Shi ya kawo Saratu Daso Kannywood a inda ya sa ta a fim din sa Feleke.

Habibu Sani: Tsohon mai shirya finafinai na Kamfanin K Films Multi Services, kuma tsohon ma’aikacin Hukumar Tarihi da Al’adun Gargajiya ta Jihar Kano, shi ne Furodusan Saki Reshe 2 da Reshe Ya Juye da Mujiya 1 da na 2. Shi ne kuma ya jagoaranci Kungiyar AHFIP a zamanin Abubakar Rabo.

Auwalu Isma’il Marshal: Tsohon Shugaban Kungiyar Tumbin Giwa da ta koma Tumbin Giwa Films, ya jagoranci shirin finafinai, yanzu kuma Shugaban Kungiyar Dattawan Kannywood.

Adamu Mohammed. Shi ne mai Kamfanin Kwabo Films, wanda ya yi fim din Kwabon Masoyi daga littafinsa mai wannan suna da kuma Dan Almajiri na 1 da na 2.

Umar Bawa Dukku: Shi ne mai Kamfanin Dukku Productions wanda ya shirya finafinan barkwannci da dama. Shi ne kuma wanda ya fara buga fim a faifan SIDI da fim din sa mai suna Zainab a lokacin ana sakin finafinai a kaset.

Hamisu Lamido Iyan Tama: Shi ne mai Kamfanin Iyan Tama Multimedia, finafinan Gashin Kuma da Kilu Ta Ja Bau, na daga cikin finafinan da kamfaminsa ya shirya, baya ga buga wakoki na sauran finafinai da kuma fito da Ali Baba Yakasai wanda ya fara buga wa Rarara kida.

Abubakar A. S. Mai Kwai: Shi ne mai Kamfanin Mai Kwai Mobies, inda ya shirya kuma ya dauki nauyin finafinai irinsu Kona Gari, Munafikin Mata da sauransu.

Abdullahi Maikano: Mazaunin garin Kaduna ne, ya yi suna a shirya finafinai a baya, ya taba zama Shugaba Kungiyar MOPPAN

Yakubu Lere: Fitaccen furodusa da ya yi fim din Wasila na 1 da na 2 a karkashin kamfaninsa na Lerawa Films da kuma wasu finafinan. Ya taba zama mai ba Gwamnan Jihar Kaduna Shawara kan Harkar Yada Labarai.

Aminu Hudu: Mai Kamfanin ALMAH Productions, tsohon furodusa ne da ke garin Jos ya yi suna a harkar sayar da kaset kafin ya koma shirin fim a shekarun 1990.

Rabi’u HRB: Shi ne mai Kamfanin HRB Films mai ofishi a Kano daga baya ya koma Kaduna. Ya yi finafinai da yawa a ciki har Gyale da kuma Abin Sirri Ne.

 Ibrahim Dahiru: Shi ne mai Kamfanin 3SP a Jos, ya yi finafinai da dama a karkashin kulawar Abubakar da kuma Shehu.

Bala Anas Babinlata: Koda yake an fi saninsa a harkar rubutu da kuma bayar da umarni, amma ya yi finafinai na kansa a karkashin kamfaninsa Babinlata Films Sarma-Sarma na daya daga cikinsu.

Hajiya A’isha Halilu: Tana daya daga cikin furudusoshi mata da ake ji da su a da.fim din Sahnafahna, daya daga cikin finafinanta da suka yi tashe a karkashin kamfaninta na Kumbo Productions.

Sani Mu’azu: Koda yake ya yi fice a shirye-shiryen talabijin inda yake fitowa a matsayin jarumi, Kamfaninsa na Lenscope Media da ke Jos ya kwanta dama a harkokin Kannywood. A baya sun yi finafinai da kuma samar da mawaka a masana’antar.

Alhaji Ibrahim Mandawari: Shi ne shugaban Kamfanin Mandawari Enterprises da ya shirya finafinai da dama irin su Zakaran Gwajin Dafi da Marainiya da Gaskiya Dokin Karfe.

Aminu Mirror: Aminu Mirror fitaccen furodusa ne a Zaria, wanda ya yi fice musamman a tsakanin 2000s, sai dai an dain jin ɗuriyarsa tun rasuwar abokinsa Ahmed S. Nuhu. Daga cikin finafinan da ya shira a Kamfanin Ijaba Productions akwai Ibro Police da Sirri ne.

Sai ya sake dawowa a fim din Gidan Badamasi mai dogon zango a matsayin Malam Zaidu.

Aminu Bizi: Shi ne Shugaban Kamfanin Bizi Productions, kuma ya shirya finafinai irinsu tsohon dan siyasa da Baba Ari ya ja da sauransu.

Ahmed Bifa: Shugaban Kamfanin Bifa Productions. Ya shirya finafinai irinsu Kyandir da Bakar fuska.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: fina finan Kannywood Hamisu Iyantama Ibrahim Mandawari kannywood a shirya finafinai a masana antar da ya shirya a karkashin

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 126

126-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da haka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Muttahhari, ko kuma cikin littafin mathnawa na maulana Jalaluddeen Rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sarir Imam Al-Hassan Almujtaba (a) diyar Fatima (s) kuma jikan manzon All..(s) na farko da muke kawo maku, idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun bayyana yadda. Imam Al-Hassan (a) tare da sahabban manzon All…(s) da dama suka fuskance Abu-Musa Al-ashari, har sai da suka fidda shi daga gidan gwamnati, sannan suka shawo kan mutanen kufa suka amince su fita yaki tare da Imam amiril muminina Aliyu dan Abi talib (a). Sannan daga karshe Imam Hassan ya fadawa mutanen kufa kan cewa, daga yanzun Urdatuh Ibn Kaab bin Thalaba al-ansari shi ne walin Kufa.

Sannan ya ce masu duk wanda yake da abin hawa ya bini mu wace wadanda kuma zasu bi ta ruwa suna iya bi.

Sannan daga karshe mun yi magana kan cewa, an yiwa Imam Al-Hassan (a) karya, dangane da shi da Mahaifinsa, Imam Ali (a), kamar yadda Tabari ya kawo a cikin tarihinsa ya ruwaito hadisin daga Saifu dan Umar Attamimi, wanda malaman da dama suna tuhumarsa da kariya da kuma kirkiro hadisai ya jinginawa manzon All..(s).

A cikin hadisin ya na cewa, Imam Hassan (a) yana umurtan mahaifinsa yayi wasu abubuwa amma yana saba masa, kama sanadiyyar haka ya fada cikin matsaloli. Kumma dukkan abubuwan sun shafi kissan Khalifa Uthman ne da kuma bai’a was hi Imam (a). Mu bayyana bayyan cewa, girmamawa da ladabi ga mahaifi da kuma limamin zamani wani al-amari ne wanda babu shakka a cikin iyalan gidan manzon All..(s) tsarkaka, don haka shi ya sa basa sabani a tsakaninsu. Wannan kuma ya nuna mana yadda musulmi da dama basu san matsayin Aliyu (a) a wajen All.. da kuma matansa da yayasa 11 masu tsarki ba.

Don haka baya da mutanen suka hadu da sauran wadanda suke tare da Imam (a). sai suka kama hanyan basra suna sauri. A lokainda ya isa wani wuri kusa da Basra wana ake kira ‘Zawiyya’ sai yayi zango a nan, sannan ya yi sallah raka’o’I 4 sannan yayi ta murgude kumatunsa a kasa yana zubar da hawaye yana addu’a, inda a ciki yana rokon All.. taimako kan wadanda suka zalunci shi, wato Talha da zubair, sannan ya roki All… ya tsare jinin musulmi da zuba a tsakaninsu.

Da ya kammala sai nana take, ya aiki Ubaidullahi dan Abbas da Zaidu dan Sauhan zuwa wajen Aisha su fada mata, kan cewa ta dakatar da zubar da jinin musulmi, ta kuma yi kokarin hada kansu. Yace masau:

{Ku fada mata, All..ya umrceki ki zauna a gidanki, kada fi fita daga gidan, kuma Lalle kin san hakan, sai dai wata jama’a ta rude ki, sai kika fito daga gidanki, sai mutane suka fada cikin bala’ii da da wahala, saboka haduwarsu da ke, abinda yafi maki alkhairi shi ne ki koma gidanki, kada ki shiga cikin jayayya da ya shafi yakin nan, to idan baki koma ba , kabi dushe wannan wutar fitina da kika kunna ba, to kuwa karshensa yaki ne, kuma za’a kashe mutane da dama saboda cikinsa, ki ji tsoron All…yak e Aisha, ki tuba zuwa ga All…, don lalle shi All..mai karban tuba ne, daga bayinsa, kuma yana yin afwa. Ana jiye maki tsoro kan son Abdullahi dan Zubair da dangin Talha, zuwa wani abinda karshensa wata ne}.

Da Aisha ta ji wannan nasir da yayi mata, dai ya fiye mata Alkhairi, ga kuma Al-ummar gaba daya. Amma ta sanya wannan nasihar bayan kunnenta, sai ta fadawa manzannin Imam (a). Lalle ni, ba zan mayarwa Aliyu dan Abitalib da wata magana ba, don ni bai kai ga hujjacewa da shi ba} gaskiyan ita ce, bata da hajjan da zata bawa Aliyu (s) a kan abinda ta aikata ba.

Sanna Imam (a) ya aikawa Talha da Zubair, yana kiransu da kawo karshen rarraba kamar yadda ya zo cikin wannan nassin.

{Bayan haka, hakika kun sani ko da kun buye shi, ni ban bukaci mutane su yi mani bai’a a matsayin Khalifa ba, su suka nemi in zama shugabansau, ban karbi bai’arsu ba sai da suka suka matsa mani da yin hakan, ku biyu din nan suna daga cikin wadanda suka zo mani da batun bai’a a gareni, kuma kuka yi mani bai’a, Kuma lalle sauran mutane basu yi mani bai’a ba, don samun iko ba, a cikin mafi yawansu, ko kuma don su sami wani abin duniya ba, idan har kun yi mani bai’a kuna masu biyayya to ku dawo ku tuba zuwa ga All..da sauri. Idan kuma kun mani bai,a ba tare da kuna so ba, to amma kun bani hujja a kanku, tare da bayyana biyayarku, sannan a dayan bangaren kuma kun dage a kan sabonku.

Na rantse da All..ba ku ne kuka fi cancantar yin takiyya ko boye abinda ke zukatanku ba,  a cikin wadanda suka yi hijira ba, ai wallah da kun ki yin bai’ar tun farko, kafin ku shigeta da ya fi maku fadi, a kan yin bai,a da kuma warware shi bayan haka ba.

Sannan kun riya cewa ni na kashe Uthman, shin tsakanina da ku, wa ye baya nan daga cikin mutanen Madina, idann har za’a luzumtawa ko wani mutum gwagwadon abinda ya aikata, Yak u dattawa biyu ku dawo daga wannan ra’ayinku, babban abinda zai sameku idan kun dawo shi ne kunya a duniya, ku tuba kafin kunya da kuma wutan Jahannama su taru gareku, wassalam}.

Amma sun ki amsa kirin Imam (a), sun ci gaba da nuna turjiya. Sanna Abdullahi dan Zubair dan Awwam ya tashi yayi magana. Kafin haka, shi yafi kowa hargitsa al-amuran Imam Ali(a) na dakatar da yaki da kuma hana zaman, lafiya, ya tare wasu mutanen Basra, yana harzukasu su yaki Imam (a). kuma shi ne ha bata dukkan shirye-shiryen Imam (a) na kada a kara zuabar da jinin musulmi, bayan wanda suka yi kafin isarsa basra.

Ga abinda Abdullahi dan zubair yake fada a lokacin: “Ya ku mutane! Lalle Aliyu dan Abitalb (a) ya kashe Khalifa Uthman da gaskiya, sannan ya tada rundunonin yaki don ya mamaye ku, ya kuma kwace birninku, ku kasance mutane, masu neman fansar jinin Khalifanku, ku kare haruminku, ku yi yaki don kare matanku da yaranku. Da kuma danginku da matsayinku da mutanenku. Shin kuna son mutanen kufa su kwace garinku? Ku yi fushi an fusatar da ku. Ku yi yaki an yakeku. Ku saurar Lallai Aliyu baya ganin wani yana tare da shi a cikin wannan al-amarin shugabanci sai shi.

Wallahi idan ya sami iko a kanku sai ya halaka addinin da duniyarku.”

Khudubar gaba dayanta a cikin da karya da kuma kokarin ingiza mutanen Basra su yaki Amirulmuminin (a). sannan shi kansa Abdullahi dan Zubair ya san cewa abinda ya fada a khudubarsa dangane da Amirul muminin (a) musamman na cewa shi ya kashe Khalifa Uthman karyace. Sai ya fadi abinda ransa ya sawwala masa ne kawai.

A lokacinda Imam Ali (a) ya ji abinda Abdullahi dan Zubair ya fada, sai ya fadawa dansa Imam Al-Hassan ya mayar masa, ko yayi masa radda.

Sai Imam Al-hassan (a) ya tashi ya yi khuduba ya godewa All..ya kuma yabe shi : Ya ku mutane, hakaki maganganin dan Zubair danagane da mahaifi na ya riske mu, kan cewa shi ya kashe Uthman, sannan ku ya ku wadanda suka yi hijira da kuma Ansar da waninsu daga cikin musulmi ku kunsan zancen Zubairu dangane da Uthman kafin a kashe shi.da kuma sunan Uthman a wajensa (a lokacin) da kuma tsokanar da yake masa. Kuma shi Talha dan’ubaidullah a lokacin, ya kafa tutarsa a kan Baitul malim (uthman yana da ransa) sannan ga shi a yau suna tuhumar mahaifina da kasashe shi. Suna aibata shi. Da muna son Magana a kansu da mun fada. Amma zancensa na cewa lalle Aliyu ya kwacewa mutane shugabancinsu, wannan shi ne hujja hujja mafi girma ga mahaifi na, ya riya cewa ya yi masa mubaya’a da  hannunsa amma bai yi masa mubaya’a da zuciyarsa ba. Hakika ya tabbatar da cewa yayi bai’a, sannan ya riya cewa bai yarda ba a cikin zuciyarsa, to ya zo da hujja kan cewa bai yarda ba, a cikin zuciyarsa, in zai iya. ?

Amma cewarsa mutanen kufa suna son shigawa mutanen basra kasarsu, menene abin mamaki na ma’abuta gaskiya, sun shigowa mutanen bata? Na rantse da All..mutanen Basra, sus an cewa zamu gamu da su a mahadarmu a ranar kiyama, Randa zamu kai kararsu a gaban All..sai ya hukunta da gaskiya a tsakamimmu, shi ne mafi alkhairin mai rarrabewa.

Amma magoya bayan Uthman, kuma, babu yaki a tsakanimmu da su, babu wata fafatawa, sai dai yakimmu da ma’abuciyar Rakumine ce, da mabiyanta.)

Da haka Imam Alhassan(a). ya mayarwa dan Zubair amma a kan zargin da yakewa babansa na kashe uthman, ya kuma tabbatar masa cewa babansa Zubair da kuma abokinsa Talha bin Ubaidullahi da kuma Aisha matar manzon All..(s) ne suka kashe Uthman, da bakunansu, babansa ya doura tutansa a kan  Baitul malin Uthman tun yana da ransa yana jiran a kasheshi don ya kwace dukiyar musulmu.

Sannan yace, yakinsu da mahayin rakumi ne don ita ta tara dangin uthman, don ta cimma burinta na nisantar da iyalan gidan manzon All.. s daga shugabancin al-ummar kakanshi.

Don haka bayan wadannan wasiku da sakonni da kuma khudubobi, da alamun babu makawa sai an ci gaba da zubar da jinni  musulmi. Don haka Imam Ali (a) ya dauki mataki na karshe, don haka zubar da jinin musulmi, idan har wannan matakin bai sami nasara ba, ba abinda ya rage in banda takobi. Wannan matakin dai shi ne kiransu zuwa ga alkur’ani mai girma wanda abin amincewa ne tsakanin dukkan bangarorin.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu na yau sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu, wassalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 125 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124 August 13, 2025 Iran: Babu Mika Kai Ga Takurawar kasashen Yamma har sai An Kawo Karshen Barazana August 13, 2025 Hukuma Mai Kula Da Sauka Da Tashin Jiragen Sama A Paris Ya Dakatar Da Wani Ma’aikacinta August 13, 2025 Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Masar Ya sake Ganawa da Aragchi Da Kuma Gorossy August 13, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe August 13, 2025 Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Jaddada Kasancewar Iran Tare Da Kasar Lebanon Koda Yaushe August 13, 2025 Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin August 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama shi da N25m na sayen kuri’u a zaɓen Kaduna
  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
  • An Gano Gawar Wani Sojan HKI Wanda Ya Kashe Kansa Saboda yakin Gaza
  • Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Iran Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wanda Ya Kai Mata Hari
  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse
  • Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 126
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124