Aminiya:
2025-05-01@04:33:49 GMT

Tsofaffin furodusoshin Kannywood da aka daina jin ɗuriyarsu

Published: 18th, March 2025 GMT

Masana’antar Kannywood ta dade tana nishaɗantar da al’umma, musamman Hausawa da sauran kabilun Arewacin Najeriya.

A makon jiya Aminiya ta ruwaito a cewa kasuwancin fina-finan ya samu koma-baya matuƙa, wanda hakan ya sa wasu suke nuna yatsa ga furodusohin yanzu kan gaza shirya fim ɗin da za a iya haskawa a Netflix da sauran manyan hanyoyin nuna fina-finai da za su samar wa masana’antar kuɗin shiga.

NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza

Wannan ya sa Aminiya ta yi waiwayen wasu furodusohin da aka daina jin ɗuriyarsu a masana’antar.

Salisu Galadanchi – Shi ne Daraktan Fim din Turmin Danya, fim na farko a Kannywood, ya yi ritaya daga aikin gwamnati a Gidan Talabijin na CTV, yana zaune a Kano.

Umar Sheikh Mohammed: Shi ne mai Kamfanin Godiya and Dan Hassan wanda ya shirya fina-finan barkwanci, shi ma ya yi nukusani.

Bala Ahmed: Ana kiransa da Bala Sarauniya saboda rawar da ya taka wajen shiryawa da gabatar da finafinan Kamafanin Sarauniya Films a Kano.

Auwalu Mohammed Sabo shi ne Furodusan Kamfanin Sarauniya Films wanda suka yi finafinan gargajiya irin su Sangaya da Daskindaridi da Linzami da Wuta da sauransu. Yanzu yana aiki a Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Ali Jindos Aneesa: Tsohon mai daukar hoto na masana’antar, wanda ya koma shirya fim. Shi ya kawo Saratu Daso Kannywood a inda ya sa ta a fim din sa Feleke.

Habibu Sani: Tsohon mai shirya finafinai na Kamfanin K Films Multi Services, kuma tsohon ma’aikacin Hukumar Tarihi da Al’adun Gargajiya ta Jihar Kano, shi ne Furodusan Saki Reshe 2 da Reshe Ya Juye da Mujiya 1 da na 2. Shi ne kuma ya jagoaranci Kungiyar AHFIP a zamanin Abubakar Rabo.

Auwalu Isma’il Marshal: Tsohon Shugaban Kungiyar Tumbin Giwa da ta koma Tumbin Giwa Films, ya jagoranci shirin finafinai, yanzu kuma Shugaban Kungiyar Dattawan Kannywood.

Adamu Mohammed. Shi ne mai Kamfanin Kwabo Films, wanda ya yi fim din Kwabon Masoyi daga littafinsa mai wannan suna da kuma Dan Almajiri na 1 da na 2.

Umar Bawa Dukku: Shi ne mai Kamfanin Dukku Productions wanda ya shirya finafinan barkwannci da dama. Shi ne kuma wanda ya fara buga fim a faifan SIDI da fim din sa mai suna Zainab a lokacin ana sakin finafinai a kaset.

Hamisu Lamido Iyan Tama: Shi ne mai Kamfanin Iyan Tama Multimedia, finafinan Gashin Kuma da Kilu Ta Ja Bau, na daga cikin finafinan da kamfaminsa ya shirya, baya ga buga wakoki na sauran finafinai da kuma fito da Ali Baba Yakasai wanda ya fara buga wa Rarara kida.

Abubakar A. S. Mai Kwai: Shi ne mai Kamfanin Mai Kwai Mobies, inda ya shirya kuma ya dauki nauyin finafinai irinsu Kona Gari, Munafikin Mata da sauransu.

Abdullahi Maikano: Mazaunin garin Kaduna ne, ya yi suna a shirya finafinai a baya, ya taba zama Shugaba Kungiyar MOPPAN

Yakubu Lere: Fitaccen furodusa da ya yi fim din Wasila na 1 da na 2 a karkashin kamfaninsa na Lerawa Films da kuma wasu finafinan. Ya taba zama mai ba Gwamnan Jihar Kaduna Shawara kan Harkar Yada Labarai.

Aminu Hudu: Mai Kamfanin ALMAH Productions, tsohon furodusa ne da ke garin Jos ya yi suna a harkar sayar da kaset kafin ya koma shirin fim a shekarun 1990.

Rabi’u HRB: Shi ne mai Kamfanin HRB Films mai ofishi a Kano daga baya ya koma Kaduna. Ya yi finafinai da yawa a ciki har Gyale da kuma Abin Sirri Ne.

 Ibrahim Dahiru: Shi ne mai Kamfanin 3SP a Jos, ya yi finafinai da dama a karkashin kulawar Abubakar da kuma Shehu.

Bala Anas Babinlata: Koda yake an fi saninsa a harkar rubutu da kuma bayar da umarni, amma ya yi finafinai na kansa a karkashin kamfaninsa Babinlata Films Sarma-Sarma na daya daga cikinsu.

Hajiya A’isha Halilu: Tana daya daga cikin furudusoshi mata da ake ji da su a da.fim din Sahnafahna, daya daga cikin finafinanta da suka yi tashe a karkashin kamfaninta na Kumbo Productions.

Sani Mu’azu: Koda yake ya yi fice a shirye-shiryen talabijin inda yake fitowa a matsayin jarumi, Kamfaninsa na Lenscope Media da ke Jos ya kwanta dama a harkokin Kannywood. A baya sun yi finafinai da kuma samar da mawaka a masana’antar.

Alhaji Ibrahim Mandawari: Shi ne shugaban Kamfanin Mandawari Enterprises da ya shirya finafinai da dama irin su Zakaran Gwajin Dafi da Marainiya da Gaskiya Dokin Karfe.

Aminu Mirror: Aminu Mirror fitaccen furodusa ne a Zaria, wanda ya yi fice musamman a tsakanin 2000s, sai dai an dain jin ɗuriyarsa tun rasuwar abokinsa Ahmed S. Nuhu. Daga cikin finafinan da ya shira a Kamfanin Ijaba Productions akwai Ibro Police da Sirri ne.

Sai ya sake dawowa a fim din Gidan Badamasi mai dogon zango a matsayin Malam Zaidu.

Aminu Bizi: Shi ne Shugaban Kamfanin Bizi Productions, kuma ya shirya finafinai irinsu tsohon dan siyasa da Baba Ari ya ja da sauransu.

Ahmed Bifa: Shugaban Kamfanin Bifa Productions. Ya shirya finafinai irinsu Kyandir da Bakar fuska.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: fina finan Kannywood Hamisu Iyantama Ibrahim Mandawari kannywood a shirya finafinai a masana antar da ya shirya a karkashin

এছাড়াও পড়ুন:

Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa

Shugaban Palasdinu da kuma kungiyar kwatar yencin falasdinawa PLO Mahmud Abbas ya nada magajinsa da kuma wasu mataimaka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran, ta bayyana cewa Abbas dan shekara 89 ya nada mataimakinsa ne bayan taron majalisar gudanarwa ta gwamnatinsa  a makon da ya gabata.

Labarin ya kara da cewa kasashen yamma da yankin sun dade suna takurawa Abbas kan ya nada mataimaki da kuma wasu mataimaka sabuda rawar da gwamnatinsa zata taka bayan yakin gaza.

A yau ne majalisar zartarwa ta amince da nada Hussein Al Sheikh a matsayin mataimakin shugaban majalisar da kuma mataimakin shugaban kasa a lokaci guda.

Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Falasdinawan WAFA, ya bayyana cewa gwamnatin Abbas ce da hakkin sa hannu a kan yarjeniyoyi da suka shafi Falasdinu, a madadin dukkan kungiyoyin Falasdinawa, banda wadanda su ka dauke da makamai suna yakar HKI, wato Hamas da kuma Jihadul Islami a Gaza.

Mr Al Sheikh, dan shekara 64 a duniya na hannun daman Abbas ne a kungiyarsa ta fatah.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano