Aminiya:
2025-07-07@01:16:43 GMT

Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka

Published: 6th, July 2025 GMT

Elon Musk, wanda ya taɓa zama mashawarcin Shugaban Amurka Donald Trump, ya ce zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa mai suna America Party.

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X (Twitter), makonni bayan wata taƙaddama da ta ɓarke tsakaninsa da Shugaban Amurka.

Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya  Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano

Musk, wanda attajirin mai kuɗi sosai, ya ce jam’iyyarsa za ta kasance wata hanya ta daban daga jam’iyyu biyu da ake da su yanzu, wato Republican da Democrat.

Amma har yanzu ba a bayyana ko hukumar zaɓen Amurka ta amince da rajistar jam’iyyar ba.

Amma Musk bai bayyana wanda zai jagoranci jam’iyyar ko irin manufofinta ba.

Tun da farko Musk ya fara maganar kafa sabuwar jam’iyya ne bayan samun saɓani da Donald Trump, wanda hakan ya kai sa ga sauka daga matsayinsa a gwamnatin Trump.

Yayin wata ƙuri’ar jin ra’ayi da ya gudanar a X, mutane miliyan ɗaya ne suka kaɗa ƙuri’a, kuma kashi 60 daga cikinsu sun amince a kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sabuwar Jam iyya Saɓani Zaɓe kafa sabuwar jam

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Babu wanda ko da a kuskure ya yi magana a kan tattaunawa da Amurka saboda tsananin fushin da al’ummar Iran ta yi

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Ismail Baqa’i ya ce dangane da tattaunawar da aka yi da Amurka, “A halin yanzu al’ummar Iran suna cikin fushi matuka, ta yadda babu wanda ya isa ya yi magana kan batun gudanar da zaman tattaunawa da Amurka ko harkar diflomasiyya.”

A cikin wata hira da gidan talabijin na Sky News, yayin da yake mayar da martani kan wata tambaya kan shirin nukiliyar Iran biyo bayan harin wuce gona da iri da Amurkawa da ‘yan sahayoniyya suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, Baqa’i ya ce: “Sun yi imani da farko dole ne su fahimci abin da ya faru, kwarai abin da ya faru shi ne wani danyen aikin wuce gona da iri da gwamnatin mamayar Isra’ila ta yi aikata kan kasar Iran, sannan kuma Amurka, kan ‘yancin kan kasar Iran da kuma ikon kasar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Togo: An Yi Kiran Sake Yin Wata Sabuwar Zanga-zanagr Kin Jinin Gwamnati
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jiran Amsar Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Shugaban Kasar Iran Ya Rattaba Hannu Kan Daftarin Dakatar Da
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?