Sayyid Husi: Idan Amurka Ta Ci Gaba Da Kai Mana Hare-hare To Muna Da Hanyoyin Gasa Mata Aya A Hannu
Published: 18th, March 2025 GMT
Shugaban kungiyar Ansarullah na kasar Yemen Sayyid Abdulmalik Husi ya bayyana cewa; Matukar Amurka ta ci gaba da kai wa Yemen hare-hare, to suna da hanyoyi da za su iya gasa mata aya a hannu masu yawa.
Sayyid Abdulmalik al-Husi ya yi ishara da yadda dubun dubatar mutanen Yemen su ka fito a cikin birnin San’aa da kuma sauran biranen kasar domin raya da tunawa da rana da aka yi yakin Badar, yana mai cea; hakan yana a matsayin wani sako ne zuwa Amurka da Isra’ila, kuma tabbas idan su ka ci gaba da kai wa Yemen hari, to muna da zabi na hanyoyin da za mu yi amfani da su domin dandana musu kudarsu.
Sayyid Husi wanda ya gabatar da jawabin dararen Ramadan mai alfarma ya kara da cewa; Sakon mutanen Yemen da su ka fito a Litinin din nan 17 ga watan Ramadana shi ne; Ba za mu taba barin abokan gaba Isra’ilawa su ci gaba da cutar da al’ummar Falasdinu, a karkashin goyon bayan Amurka ba.”
Shugaban na Ansarullah ya kuma yi Magana akan yadda abokan gaba Isra’ilawa suke ci gaba da hana shigar da kayan agaji zuwa yankin Gaza, wanda babban laifi ne da bai kamata a yi shiru a sa musu idanu ba.”
Haka nan kuma ya kara da cewa; Matakin da mu ka dauka na farko, amma idan har aka ci gaba, yunwa ta kara takurawa Falasdinawa, to matakin da za mu dauka zai fi na yanzu.”
Danagne da martanin da su ka kai wa jigin dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea”, Sayyid Abdulmalik al-Husi ya yi ishar da yadda jiragen yakin na Amurka su ka kara yin nisa zuwa kilo mita 1300, domin tsoron hare-haren sojojin Yemen.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
Daga Usman Muhammad Zaria
Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya yaba da gagarumin cigaba a harkar noma da Gwamna Umar Namadi ya samar cikin shekaru biyu kacal na mulkinsa.
Ya bayyana haka ne a masarautar Gumel cikin Jihar Jigawa, yayin kaddamar da sabon masallacin Juma’a da Gidauniyar Kashim Shettima ta gina a matsayin wani ɓangare na bikin zagayowar cikar Sarkin Gumel shekaru 45 a kan karaga.
A cewarsa, abin sha’awa ne yadda Gwamna Umar Namadi ya mayar da harkar noma a jihar Jigawa zuwa ta zamani cikin shekaru biyu kacal.
Ya jinjina wa Gwamnan da al’ummar Jihar Jigawa bisa wannan ci gaba mai armashi.
Kashim Shettima ya kara taya Sarkin Gumel, Alhaji Muhammadu Sani, murnar cika shekaru 45 a matsayin Sarkin Gumel, tare da yi masa fatan alkhairi.
Ya tabbatar da ci gaba da jajircewar Gidauniyar Kashim Shettima wajen inganta rayuwar ‘yan Najeriya.
A jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya yaba wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa kaddamar dadMasallacin.
Ya kuma taya Sarkin Gumel murnar cika shekaru 45 a kan karaga, tare da yi masa fatan alheri.
Shi ma a nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jinjina wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa gina Masallacin Juma’ar.
Namadi ya kuma yaba da jinjinar da VP ya yi kan sauyin da aka samu a harkar noma ta Jigawa, yana mai alkawarin cewa za a cigaba da kara himma a bangaren noma da ma dukkan ababen da za su ciyar da jihar gaba.
Gwamnan ya kara jinjina wa Mai Alfarma Sarkin Musulmi da sauran manyan baki bisa halartar taro.