Sayyid Husi: Idan Amurka Ta Ci Gaba Da Kai Mana Hare-hare To Muna Da Hanyoyin Gasa Mata Aya A Hannu
Published: 18th, March 2025 GMT
Shugaban kungiyar Ansarullah na kasar Yemen Sayyid Abdulmalik Husi ya bayyana cewa; Matukar Amurka ta ci gaba da kai wa Yemen hare-hare, to suna da hanyoyi da za su iya gasa mata aya a hannu masu yawa.
Sayyid Abdulmalik al-Husi ya yi ishara da yadda dubun dubatar mutanen Yemen su ka fito a cikin birnin San’aa da kuma sauran biranen kasar domin raya da tunawa da rana da aka yi yakin Badar, yana mai cea; hakan yana a matsayin wani sako ne zuwa Amurka da Isra’ila, kuma tabbas idan su ka ci gaba da kai wa Yemen hari, to muna da zabi na hanyoyin da za mu yi amfani da su domin dandana musu kudarsu.
Sayyid Husi wanda ya gabatar da jawabin dararen Ramadan mai alfarma ya kara da cewa; Sakon mutanen Yemen da su ka fito a Litinin din nan 17 ga watan Ramadana shi ne; Ba za mu taba barin abokan gaba Isra’ilawa su ci gaba da cutar da al’ummar Falasdinu, a karkashin goyon bayan Amurka ba.”
Shugaban na Ansarullah ya kuma yi Magana akan yadda abokan gaba Isra’ilawa suke ci gaba da hana shigar da kayan agaji zuwa yankin Gaza, wanda babban laifi ne da bai kamata a yi shiru a sa musu idanu ba.”
Haka nan kuma ya kara da cewa; Matakin da mu ka dauka na farko, amma idan har aka ci gaba, yunwa ta kara takurawa Falasdinawa, to matakin da za mu dauka zai fi na yanzu.”
Danagne da martanin da su ka kai wa jigin dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea”, Sayyid Abdulmalik al-Husi ya yi ishar da yadda jiragen yakin na Amurka su ka kara yin nisa zuwa kilo mita 1300, domin tsoron hare-haren sojojin Yemen.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram sun kai sabbin hare-hare a wasu yankunan Borno da Yobe
An zargi mayaƙan Boko Haram da ISWAP da kai hare-hare wasu yankuna biyar da ke Jihohin Borno da Yobe.
Sun kai hare-haren ne garuruwan Mafa, Dikwa, Marte, da Ajiri a Jihar Borno, da kuma Katarko a Jihar Yobe.
Jami’an tsaro sun kama Sowore saboda shirya zanga-zanga DSS ta cafke mutum 3 kan zargin sayar wa ’yan bindiga makamai a KadunaRahotanni sun bayyana cewa ’yan ta’addan sun fara kai hari wani shingen sojoji da ke Mafa, sannan suka sace makamai da sabbin babura da sojoji ke amfani da su.
Wata majiyar tsaro ta ce: “Sun zo da yawa kuma ɗauke da muggan makamai. Sun sace makamai da baburanmu. Yawansu dana gani abun mamaki ne.”
Ba a tabbatar da adadin sojojin da suka rasu ba, amma wani jami’in tsaro ya tabbatar da cewa sun kashe ’yan ta’adda da yawa a yayin artabun.
Wani mazaunin yankin, ya ce babu wanda aka kashe daga cikin mutanen gari, amma ’yan ta’addan sun sace kayan abinci da sauran kayayyaki, sannan suka ƙone wasu motoci.
“Lamarin ya faru ne misalin ƙarfe 11 na daren ranar Laraba. ’Yan ta’addan sun fara kai hari shingen sojoji inda matafiya ke jiran a buɗe musu hanya domin su ci gaba da tafiyarsu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa mayaƙan sun kai harin a motoci huɗu ɗauke da bindigogi da kuma babura sa.a da 100, ɗauke da makamai.
Sun kuma kai makamantan waɗannan hare-haren a Marte, Dikwa, Ajiri duk a Jihar Borno, da kuma Katarko a Jihar Yobe.