Shugaban kungiyar Ansarullah na kasar Yemen Sayyid Abdulmalik Husi ya bayyana cewa; Matukar Amurka ta ci gaba da kai wa Yemen hare-hare, to suna da hanyoyi da za su iya gasa mata aya a hannu masu yawa.

Sayyid Abdulmalik al-Husi ya yi ishara da yadda dubun dubatar mutanen Yemen su ka fito a cikin birnin San’aa da kuma sauran biranen kasar domin raya da tunawa da rana da aka yi yakin Badar, yana mai cea; hakan yana a matsayin wani sako ne zuwa Amurka da Isra’ila, kuma tabbas idan su ka ci gaba da kai wa Yemen hari, to muna da zabi na  hanyoyin da za mu yi amfani da su domin dandana musu kudarsu.

 Sayyid Husi wanda ya gabatar da jawabin dararen Ramadan mai alfarma ya kara da cewa; Sakon mutanen Yemen da su ka fito a Litinin din nan 17 ga watan Ramadana shi ne; Ba za mu taba barin abokan gaba Isra’ilawa su ci gaba da cutar da al’ummar Falasdinu, a karkashin goyon bayan Amurka ba.”

Shugaban na Ansarullah ya kuma yi Magana akan yadda abokan gaba Isra’ilawa suke ci gaba da hana shigar da kayan agaji zuwa yankin Gaza, wanda babban laifi ne da bai kamata a yi shiru a sa musu idanu ba.”

Haka nan kuma ya kara da cewa; Matakin da mu ka dauka na farko, amma idan har aka ci gaba, yunwa ta kara takurawa Falasdinawa, to matakin da za mu dauka zai fi na yanzu.”

Danagne da martanin da su ka kai wa jigin dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea”, Sayyid Abdulmalik al-Husi ya yi ishar da yadda jiragen yakin na Amurka su ka kara yin nisa zuwa kilo mita 1300, domin tsoron hare-haren sojojin Yemen.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare
  • Amurka Ta Ce: Shugaban Rikon Kwarayar Siriya Al-Julani Ya Yi Alkawarin Cewa Ba Zai Cutar Da Tsaron Isra’ila Ba