HausaTv:
2025-11-02@21:33:37 GMT

 Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda

Published: 6th, July 2025 GMT

Raundunar sojan jamhuriyar Nijar sun sanar da cewa, an kashe  sojoji 10 da kuma jikkata wasu 15 a wasu hare-hare biyu da masu dauke da makamai su ka kai a yankin Telaberi da kudu masu yammacin kasar.

Yankin Telaberi dai yana cikin yankunan da masu dauke da makamai su ka fara kai hare-hare saboda kusancinta da iyakokin kasashen Mali da Burkina Faso.

Bayanin na sojojin kasar ta Jamhuriyar Nijar wanda kafafen watsa labarun kasar su ka watsa ya kunshi cewa; Daruruwan masu dauke da bindiga sun kai hare-hare a kan sansanonin soja biyu da suke a yankin Telaberi da hakan ya yi sanadiyyar kashe sojoji 10 da kuma jikkatar wasu 15.”

Sai dai kuma sanarwar ta ce, sojojin sun yi nasarar kashe 41 daga cikin maharan.

A watan da ya shude ma dai kasar ta Nijar ta fuskanci hare-hare masu muni. Daga ciki da akwai wani kwanton bauna da aka yi wa sojoji da garin Agadas wanda ya ci rayukan 11 daga cikinsu. Haka nan kuma an kashe fararen hula 40 a wasu jerin hare-hare a fadin kasar a shekarar da ta gabata a kusa iya da Burkina Faso.

Tun daga 2015 ne dai sojojin kasar ta Nijar suke fuskantar hare-haren ta’addanci a cikin yankuna mabanbanta, musamman a yankunan da suke kan iyaka.

Yankin tafikin Chadi dai daya daga yankuann da suke da iyaka da Najeriya, Kamaru da Chadi, wanda yake da maboyar ‘yan kungiyoyin Bokoharam da kuam ISIS.

Kasashe uku da yammacin Afirka da su ka  kafa tsarin Kwanfaderaliyya da su ne; Mali, Nijar da Burkina Faso, suna Shirin kafa rundunar soja ta hadaka mai mayaka 5000 domin fuskantar ‘yan ta’adda da tsararrun laifuka. Sanarwar hakan dai ta fito ne daga bakin ministan tsaron Nijar Salihu Mudi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.

 

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori November 1, 2025 Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar