HausaTv:
2025-07-06@22:03:44 GMT

 Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda

Published: 6th, July 2025 GMT

Raundunar sojan jamhuriyar Nijar sun sanar da cewa, an kashe  sojoji 10 da kuma jikkata wasu 15 a wasu hare-hare biyu da masu dauke da makamai su ka kai a yankin Telaberi da kudu masu yammacin kasar.

Yankin Telaberi dai yana cikin yankunan da masu dauke da makamai su ka fara kai hare-hare saboda kusancinta da iyakokin kasashen Mali da Burkina Faso.

Bayanin na sojojin kasar ta Jamhuriyar Nijar wanda kafafen watsa labarun kasar su ka watsa ya kunshi cewa; Daruruwan masu dauke da bindiga sun kai hare-hare a kan sansanonin soja biyu da suke a yankin Telaberi da hakan ya yi sanadiyyar kashe sojoji 10 da kuma jikkatar wasu 15.”

Sai dai kuma sanarwar ta ce, sojojin sun yi nasarar kashe 41 daga cikin maharan.

A watan da ya shude ma dai kasar ta Nijar ta fuskanci hare-hare masu muni. Daga ciki da akwai wani kwanton bauna da aka yi wa sojoji da garin Agadas wanda ya ci rayukan 11 daga cikinsu. Haka nan kuma an kashe fararen hula 40 a wasu jerin hare-hare a fadin kasar a shekarar da ta gabata a kusa iya da Burkina Faso.

Tun daga 2015 ne dai sojojin kasar ta Nijar suke fuskantar hare-haren ta’addanci a cikin yankuna mabanbanta, musamman a yankunan da suke kan iyaka.

Yankin tafikin Chadi dai daya daga yankuann da suke da iyaka da Najeriya, Kamaru da Chadi, wanda yake da maboyar ‘yan kungiyoyin Bokoharam da kuam ISIS.

Kasashe uku da yammacin Afirka da su ka  kafa tsarin Kwanfaderaliyya da su ne; Mali, Nijar da Burkina Faso, suna Shirin kafa rundunar soja ta hadaka mai mayaka 5000 domin fuskantar ‘yan ta’adda da tsararrun laifuka. Sanarwar hakan dai ta fito ne daga bakin ministan tsaron Nijar Salihu Mudi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da labarin da ministan harkokin wajen kasar Jamus ya watsa dangane da shirin Nukliyar kasarsa ya kuma kara da cewa labarin jabu ne.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X . Ya kuma yi watsi da zancen ministan harkokin wajen kasar Jamus wanda yake cewa, jinginar da aiki tare da hukumar makamashin nukliya ta duniya wato IAEA wanda JMI ta yi,  ya na nuna cewa ba wanda zai bincika ayyukanta na makamashin nukliya ba, kuma ta rufe kofar tattaunawa Kenan.

Aragchi ya bayyana cewa wannan ba haka bane, saboda shirin nukliyar kasar Iran a halin yanzu ya na karkashin majalisar koli ta tsaron kasar Iran ne, don haka ita ce zata fayyece yadda huldar shirin zai kasance tare da hukumar IAEA. Sannan Iran bata fice daga yarjeniyar NPT ba.

Kasar Jamus dai tana goyon bayan hare=hare da HKI da AMurka suka kaiwa JMI a yakin kwanaki 12, dagan  cikin harda hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar. Ya ce aiki ne da bai dace ba wacce JKI ta yi madadin kasashen yamma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 41 a Nijar
  • Jaridar Telegraph: Makaman Iran Masu Linzami Sun Sauka Kai Tsaye Akan  Cibiyoyin Sojan Isra’ila Guda 5  
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci
  •   Gaza: Fiye Da Falasdinawa 17 Ne Su Ka Yi Shahada Ayau Juma’a