Alƙalin kotun, Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu, ta bayar da umarnin kama Lawal tare da ɗage shari’ar zuwa ranar 6 ga watan Mayu.

A wata shari’a daban, kotun ta kuma bayar da umarnin kama Jibrilla Muhammad, tsohon Manajan Darakta na Kamfanin Zuba Jari da Kadarorin Kano (KSIP), bisa zargin ɓatan Naira miliyan 212.

4.

A gefe guda ta sake ɗage zaman wannan shari’a saboda abokin shari’ar tasa, Dauda Sheshe, har yanzu bai karɓi sammaci ba.

An ɗage shari’arsu zuwa ranar 29 ga watan Afrilu.

Dukkanin waɗannan shari’u na da alaƙa da zargin karkatar da kuɗaɗen jama’a yayin da suke rike da muƙaman gwamnati.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tsohon Kwamishina

এছাড়াও পড়ুন:

Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Katsina ta sanar cewa, za a fara jigilar maniyyatan jihar a ranar Lahadi 18 ga wannan wata na Mayu, 2025, zuwa Ƙasa Mai Tsarki.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Alhaji Badaru Bello Karofi, ya shaida wa wakilinmu, cewa maniyyatan da suka fito daga Malunfashi da Bakori, Ƙanƙara, Dandume, Ƙafur da Ɗanja sune rukunin farko da ake sa ran za su tashi daga filin sauka da tashin jiragen sama na Umaru Musa da ke cikin babban birnin jihar.

Tun farko sai da jagoran mahajjatan jahar, wanda kuma shi ne mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruk Joɓe ya bayyana cewar, gwamnatin jihar ta ɗauki duk wasu matakan da suka wajaba tun daga gida har zuwa Ƙasa Mai Tsarki domin ganin cewa mahajjatan jihar sun samu duk wata kulawa a hukumance don gudanar da aikin ibadar cikin jin daɗi da walwala.

Sai dai Amirul Hajjin ya ja hankalin maniyatan da su kiyaye duk wata doka, tun daga nan gida har a can Saudiyya inda suke ɗaukar hukunci mai tsanani ga wanda ya saɓa, musamman shiga da duk wani nau’in abin da zai sa maye da sauransu.

Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure ISWAP ta yi wa manoma 15 yankan rago a Borno

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai
  • An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja
  • Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta
  • An yi zanga-zanga zagayowar ranar ‘’Nakba’’ a sassan duniya da dama
  • Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
  • Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano
  • Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya
  • Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jihar Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu
  • Chadi: An Kama Tsohon Fira Minista Kuma Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasa
  • An kama wasu da haramtaccen buhunan takin zamani 20 a Borno