Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa

এছাড়াও পড়ুন:

Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila

Rahotanni sun bayyana cewa wani ƙazamin faɗa ya barke tsakanin wata ƙabilar Palasɗinawa masu ɗauke da makamai da ƙungiyar Hamas a yankin zirin Gaza bayan an kulla yarjejeniyar zaman lafiya da Isra’ila.

A ranar Litinin da aka fara musayar fursunoni tsakanin Hamas da Isra’ila ne rahotanni suka ɓulla game da faɗan da ya ɓarke tsakanin mayaƙan Hamas da ƙabilar Doghmush a ranar Lahadi.

Wani jami’in Hamas ya bayyana cewa an samu asarar rayuka daga kowane ɓangare a yayin musayar wutan daga misalin ƙarfe 9.30 na dare ranar Lahadi.

Wani mazaunin yankin Sebra da ke Birnin Gaza, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa “Mayaƙan Hamas kimanin 200 ne suka zo aka fafata da su, har sai da suka murƙushe ’yan ƙabilar Doghmush.

Issa Bakary Tchiroma ne ya lashe zaɓen Kamaru —’Yan adawa NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?

“Wasu ’yan ƙabilar da mayaƙan Hamas sun rasu a yayin artabun,” in ji shi yana mai neman a dakata sunansa saboda dalilan tsaro.

Wata majiya daga ma’aikatar harkokin cikin gida ta Hamas ta zargi ’yan ƙabilar da yi wa sojojin Isra’ila aiki kuma sun kashe mutane da dama, ta ƙara da cewa an tsare mutum shiga daga danginsu.

Iyalan sun musanta zargin da ake musu na yi wa Isra’ila aiki, amma sun amsa cewa sun kai wasu farmaki ba tare da yin ƙarin haske ba.

Sun kuma zargi Hamas da kai musu hari barkatai, kamar yadda AFP ya ruwaito.

Shugaban kabilar, Abu al-Hassan Doghmush, ya wallafa a Facebook cewa abin “ya kai matakin da in dai kai dan ƙabilarmu ce to a iya harbin ka a ƙafa koma kone maka gida.”

Tun da Hamas ta kwace iko a yankin Gaza a 2007 ta sha fama da kabilu da ƙungiyoyi masu ɗaukar makamai.

A ranar Lahadi ne kungiyar ta sanar da afuwa ga duk kungiyoyin masu laifi, waɗanda ba su aikata kisa a lokacin yaƙin ƙasar da Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa za ta tantance Amupitan a ranar Alhamis
  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • ’Yan Majalisar Tarayyar Kaduna 3 sun sauya sheka zuwa APC
  • Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu
  • Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila
  • Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista