Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; Dukkanin batutuwan  da Musulunci da kuma al’kur’ani maigirma suke bijiro da su, sun ginu ne akan ginshikin gaskiya da kuma adalci.

Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa; Idan har wadannan ginshikan biyu su ka zama ana aiki da su a cikin al’umma, to za a sami shiriya.

Shugaba Mas’ud Fizishkiyan ya kuma ce; A wannan lokacin muna da bukatuwa da koyar da dalibai da ‘ya’yanmu domin su kai ga mataki na koli na ilimi da kuma kyawawan halaye, ta yadda za su zama karfin madogara da hikima da kyawawan halaye a cikin al’umma.

Shugaban na kasar Iran ya kuma ce: Abubuwan da musulunci da kuma al’kur’ani suke bijiro da su, sun ginu ne akan ginshikai biyu da su ne  gaskiya da kuma adalci a cikin dukkanin fagage.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya buƙaci Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya daina siyasantar da harkar tsaro a jihar.

Ya ce kamata ya yi gwamnan ya mayar da hankali kan matsalolin da ke damun jihar.

Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali

Barau, ya yi wannan bayani ne bayan gwamnatin Kano ta zarge shi da yin magana inda ya nemi gwamnatin ta mayar da hankali kan tsaro.

Ya ce matsalolin tsaro a ƙasar nan, ciki har da hare-haren ’yan bindiga a wasu yankunan Kano, suna buƙatar haɗin kai daga kowa.

A cikin wata sanarwa daga mai taimaka masa, Ismail Mudashiru, ya fitar, Barau ya ce zargin gwamnatin ba gaskiya ba ne.

Ya ƙalubalanci gwamnatin ta nuna bidiyon da ya yi maganar da za ta iya haddasa matsalar tsaro.

Ya ce wannan zargi ƙarya ne kuma na da nufin ɓata masa suna.

Ya ƙara da cewa bai taɓa yin wata magana da za ta kawo tangarɗa ga harkar tsaro ba.

A maimakon haka, ya ce yana aiki tare da sauran jami’ai domin inganta tsaro a Kano da sauran sassan Najeriya.

Barau, wanda shi ne Mataimakin Kakakin ECOWAS, ya buƙaci Gwamna Abba da ya “farka daga bacci” ya jagoranci jihar yadda ya kamata.

Ya ce a baya Kano na gogayya da Legas wajen ci gaba, amma rashin kyakkyawan shugabanci ya janyo mata koma baya.

Ya ce ya bai wa rundunonin ’yan sanda motocin aiki, ya bai wa jami’an ’yan sanda babura a Kano ta Arewa, sannan ya gyara wasu sassan hedikwatar ’yan sanda ta Kano.

Haka kuma, ya gina ofisoshin ’yan sanda a wurare daban-daban, ya tallafa wa hukumar DSS, sannan ya taimaka wajen kafa makarantu na horar da jami’an NSCDC, Hukumar Ayyukan ’Yan Sanda, da Hukumar Shige da Fice a wasu yankunan Kano.

Ya ce ya sanya fitilu masu amfani da hasken rana a yankinsa domin taimaka wa zirga-zirga da daddare.

A cewarsa, waɗannan ayyukan suna nuna irin gudunmawar da yake bayarwa wajen inganta tsaro, don haka ya kamata gwamnatin jihar ta yi koyi da shi maimakon ɓata masa suna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • AU ta dakatar da Guinea-Bissau daga zama mamba a cikinta bayan juyin mulkin sojoji