Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; Dukkanin batutuwan  da Musulunci da kuma al’kur’ani maigirma suke bijiro da su, sun ginu ne akan ginshikin gaskiya da kuma adalci.

Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa; Idan har wadannan ginshikan biyu su ka zama ana aiki da su a cikin al’umma, to za a sami shiriya.

Shugaba Mas’ud Fizishkiyan ya kuma ce; A wannan lokacin muna da bukatuwa da koyar da dalibai da ‘ya’yanmu domin su kai ga mataki na koli na ilimi da kuma kyawawan halaye, ta yadda za su zama karfin madogara da hikima da kyawawan halaye a cikin al’umma.

Shugaban na kasar Iran ya kuma ce: Abubuwan da musulunci da kuma al’kur’ani suke bijiro da su, sun ginu ne akan ginshikai biyu da su ne  gaskiya da kuma adalci a cikin dukkanin fagage.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sake aike wa Majalisar Dattawa ƙarin sunayen mutum 32 domin tantance su a matsayin jakadu.

Sunayen sun haɗa da manyan mutane kamar tsohon shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Femi Fani-Kayode, da Reno Omokri.

Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe

An raba sunayen zuwa kashi biyu; na farko yana ɗauke da sunan mutum 15 waɗanda suke da gogewar aikin jakadanci da kuma waɗanda ba su gogewar aikin jakadanci mutim 17.

Wasu daga cikin fitattu da suka shiga jerin sun haɗa da tsofaffin gwamnonin kamar Ifeanyi Ugwuanyi da Victor Okezie Ikpeazu, matan tsofaffin gwamnoni kamar Angela Adebayo da Florence Ajimobi, da kuma Sanata Jimoh Ibrahim.

Bayan tantancewa, za a tura jakadun zuwa ƙasashe irin su China, Indiya, Kanada, UAE, Afrika ta Kudu, da Kenya.

Sauran wuraren sun haɗa da manyan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa kamar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), UNESCO, da Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).

Za a bayyana inda za a tura kowane, bayan Majalisar Dattawa ta tantance su.

A makon da ya gabata ne, Tinubu ya tura sunayen mutum uku da ake sa ran tura su Amurka, Birtaniya ko Faransa.

Shugaban ya ce za a sake fitar da ƙarin sunayen jakadu nan ba da jimawa ba.

Wannan mataki na cikin shirin Tinubu na karfafa hulɗar diflomasiyya ta hannun ƙwararru da gogaggun mutane don wakiltar Najeriya a ƙasashen waje.

Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta fara tantance su cikin makonni masu zuwa, kafin su kama aiki.

Masu sharhi kan sha’anin siyasa suna ganin waɗanda aka zaɓo ƙwararru ne kuma za su taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasar gida da waje.

Da dama na ganin cewa waɗannan naɗe-naɗen za su iya taka rawa wajen tsara sabuwar hanyar hulɗa da ƙasashen waje da manufofin diflomasiyyar Najeriya a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • AU ta dakatar da Guinea-Bissau daga zama mamba a cikinta bayan juyin mulkin sojoji
  • Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban