Leadership News Hausa:
2025-07-07@01:47:08 GMT

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Published: 7th, July 2025 GMT

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Tawagar ƙwallon ƙafar mata ta Nijeriya ta fara gasar ƙwallon ƙafa ta mata ta ƙasashen Afirika da kafar dama, bayan lallasa ƙasar Tunisia da ci 3-0 a wasan farko da suka buga yau Lahadi a filin wasa na Prince Moulay Abdellah.

Asisat Oshoala da Rinsola Babajide da Chinwendy Ihezuo ne suka jefa kwallayen da suka yi sanadiyar samun nasarar ‘yan matan, yanzu Nijeriya ta dare teburin rukunin ‘B’ wanda ke ɗauke da ƙasashen Algeria da Botswana da Tunisia da Nijeriya.

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

‘Yan matan da Madugu ke jagoranta za su haɗu da ƙasar Botswana a wasa na biyu, Nijeriya ce ƙasar da tafi lashe wannan gasar a tarihi yayin da ta lashe sau 9, Super Falcons kamar yadda ake kiransu tana fatan ganin sun dawo da wannan kofi zuwa gida Nijeriya, domin ragewa ‘yan ƙasar raɗaɗin rashin nasara a wasan ƙarshe na gasar kofin ƙasashen Afirika da aka buga a ƙasar Cote d’voire.

Yanzu dai tawagar za ta yi ƙoƙarin ganin ta ci gaba da samun nasarori yayin da take shirin tunkarar wasansu na gaba da ƙasar Botswana a ranar Alhamis, wannan nasarar ta aike da saƙo ƙarara ga sauran ƙasashen da ke buga gasar, wanda ke nuna matsayinsu na kasancewa kan gaba a gasar ƙwallon ƙafa ta mata a Afirka, da kuma ƙarfafa matsayinsu a matsayin ƙasar da ta fi samun nasara a tarihin WAFCON.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƙwallon mata Nijeriya Tunusiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 41 a Nijar

Dakarun sojin Nijar sun samu nasarar kashe ’yan ta’adda 41 a yayin wasu tagwayen hare-hare da aka kai musu ranar Juma’a a yammacin ƙasar.

A cikin wata sanarwa, Ministan Tsaron Nijar, Janar Salifou Modi ya ce hare-haren ta’addancin da ɗaruruwan ’yan ta’adda suka kai a lokaci guda, sun auku ne a yankunan Bouloundjounga da Samira a Ƙaramar Hukumar Gotheye.

Sanarwar da aka karanto a tashar talabijin ta ƙasar ta ƙara da cewa an yi asarar dakarun ƙasar 10, kana wasu 15 suka ji rauni a sakamakon wannan hari.

Yankin Gotheye yana kusa da iyakar Nijar da Mali da Burkina Faso kuma yanki ne da ya daɗe yana fuskantar hare-hare daga ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi.

Ƙauyen Samira na da kamfanin hakar zinare daya tilo a Nijar. Takwas daga cikin ma’aikatan kamfanin sun mutu a cikin watan Mayu lokacin da motarsu ta taka bam a gefen hanya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford
  • Muhimman Kamfanonin Jiragen Sama A Duniya Sun Farfado Da Zirga-Zirgaf Zuwa Iran
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 41 a Nijar
  • Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata
  • Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila
  • Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
  • “ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”