Aminiya:
2025-10-15@02:32:24 GMT

NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan

Published: 18th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Mallakar Muhalli na ɗaya daga cikin burin kowanne ɗan Najeriya.

Sai dai wannan buri a mafi yawan lokacin baya cika musamman ga masu matsakaitan samu.

Ƙananan ma’aikata da mafi ƙarancin albashin su yake naira dubu saba’in ba zai ciyar da su, ko tufatar da su ba, ballantana har su yi tunanin mallakar muhalli nasu na ƙashin kansu.

Sai dai masana na bayyana cewa marasa karfin ma na iya mallakan nasu muhallin daidai ruwa daidai tsaki.

NAJERIYA A YAU: Guraben Ayyukan Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan hanyoyin da mai ƙaramin ƙarfi zai bi don mallakar muhalli a Najeriya.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU) ta mayar da martani kan barazanar gwamnatin tarayya ta “ba aiki, ba a biya”, tana mai cewa ba za ta bari a tsoratar da ita da irin wannan gargaɗi ba. Shugaban ASUU, Chris Piwuna, ya bayyana haka a wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels a shirin Politics Today a ranar Litinin.

Piwuna ya ce ASUU ta tsaya tsayin daka tare da sauran ƙungiyoyin Malamai kamar CONUA, da NAMDA, da SSANU, da NASU, wajen goyon bayan yajin aikin da ke gudana. Ya zargi Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, da ƙoƙarin rarraba malamai ta hanyar yin alƙawarin biyan wasu ma’aikata albashi. “Ya na ƙoƙarin rarraba kan mu, amma kan mu a haɗe yake. Babu wanda zai iya tsoratar da mu,” in ji shi.

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi  ASUU Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwanaki 14 Don Biyan Buƙatunta

Shugaban ASUU ya kuma shawarci Ministan Ilimi da ya maida hankali wajen warware rikicin maimakon yin barazana. “Ya kamata ya karkata kan magance wannan matsalar. Idan kuma ya ci gaba da bin wannan hanyar ta barazana, zai gaza,” Piwuna ya ƙara da cewa.

Duk da matsayinta mai tsauri, ASUU ta bayyana cewa tana shirye don tattaunawa da gwamnati. Piwuna ya ce sun samu kiran Ministar Ƙwadago, wadda ta bayyana cewa an umurce ta da shiga tsakani don warware rikicin. “ASUU a shirye take, muna son tattaunawa don kawo ƙarshen wannan ƙwan gaba ƙwan baya,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano October 13, 2025 Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025 Manyan Labarai Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba
  • An Kara Zaburar Da ‘Yan Arewa Game Da Muhimmancin Mallakar Katin Zabe
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Yadda Ake Gurasa Ta Semovita
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta