HausaTv:
2025-07-06@21:05:24 GMT

Sheikh Kassim: Mayakan Hizbullah Mazajen Fagen Daga Ne

Published: 6th, July 2025 GMT

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’ima Kassim ya bayyana cewa; Dakarun Hizbullah mazajen fagen daga ne da ba su karbar kankanci.

Sheikh Na’im Kassim wanda ya gabatar da jawabi a wurin babban taron Ashura a ungiyar Dhahiya dake birnin Beirut, ya bayyana cew; Yaki na tsaron kasa zai ci gaba saboda mun yi Imani da ‘yanto da kasa, kuma wajibi ne akansu, ko da kuwa an dauki lokaci mai tsawo sannan kuma sadaukar da kai ya yawaita.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Isra’ila abokiyar gaba tana ci gaba da mamaye yankuna 5 na Lebanon, don haka babu yadda za a yi mu mika kai.” Haka nan kuma ya yi tambayar cewa; Ta yaya za a tsammaci za mu ki tsayuwar daka a gaban wannan abokin gfabar wanda yake ci gaba da mamaye kasa da kuma kisa?

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa; gwagwarmaya za ta ci gaba, kuma zuriya mai zuwa za su dora daga inda aka tsaya.”

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce:  Za mu kare gwagwarmayar da mutane masu yawa su ka sadaukar da kawunansu akanta, domin wannan gwagwarmaya ce ta Imam Musa Assadar, kuma ta Sayyid Hassan Nasrallah shugaban shahidan wannan al’umma.”

Da yake Magana akan yadda HKI take keta wutar yaki, Sheikh Na’im Kassim ya ce; yawan keta wutar yakin Isra’ila ya kai dubban gomomi, ya kuma kara da cewa; Batun da ake yi na wata sabuwar yarjejeniya ba zai sa mu mika wuya ba, abinda ya kamata shi ne a fada wa abokan gaba cewa; Su daina keta wutar yaki, sannan kuma gwgawarmaya tana cikin hanyoyin magance matsalar da ake fuskanta.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Sojojin kasarsa sun koya wa ‘yan sahayoniyya masu wuce gona da iri babban darasi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, a jawabin da ya gabatar a taron kolin kungiyar Hadin Gwiwar Tattalin Arziki ta ECO da aka gudanar a kasar Azarbaijan a yau Juma’a, ya jaddada cewa: Sojojin kasar Iran bisa doka mai lamba 51 na yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya  sun kare al’ummar Iran da mutuncin kasar da cikakken ikonta a yakin da aka yi a baya-bayan nan, kuma sun koyar da masu wuce gona da iri darasi mai girma da kuma dakile yaduwar yaki a wannan yanki.

A yayin taron koli karo na 17 na kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO da aka gudanar a yammacin yau Juma’a, Pezeshkian ya yi Allah wadai da harin da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya ta kai kan kasar Iran, yana mai cewa: Wannan gwamnatin ta fara ne da keta haddin ka’idoji da dokokin kasa da kasa da suka hada da Mataki na 2 sakin layi na 4 na Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya, sannan yakin ci gaba da taimakon sojojin Amurka masu dauke da dabi’ar zalunci kan Iran.

Shugaban Iran ya kara da cewa: A cikin kwanaki 12 na hare-haren wuce gona da irin, an aiwatar da wasu munanan laifuka zalunci kan sojojin da ba sa kan aikinsu da malaman jami’a da talakawan kasa da cibiyoyin makamashin nukiliya na zaman lafiya da suke karkashin kulawar hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa, da kuma kayayyakin more rayuwa.”

Haka nan kuma yayin da yake ishara da irin dimbin hasarar rayukan bil’adama da zaluncin yahudawan sahayoniyya ya janyo kan al’ummar Iran, shugaban ya ce: A bisa ka’ida ta 51 na kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya, sojojin kasar Iran sun taka rawa wajen kare halaltacciyar kasar Iran, ikon da amincin kasa, da cikakken ‘yancin kasa tare da koyar da maharan darasi mai tsauri, da kuma hana yaduwar wannan yanki a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Babban Mufti Na Masarautar Oman Ya Yi Kakkausar Suka Kan Masu Son Kulla Alaka Da H.K.Isra’ila
  • Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
  • Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran
  •  Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta