Kakakin gwamnatin kasar Iran ta bayyana cewa: Duk wanda ya canza sunan Tekun Fasha, tabbas ya jahilci tarihin dubban shekaru na Iran

Mai magana da yawun gwamnatin Iran Fatimah Mohajerani ta yi tsokaci kan rahotannin da suke cewa: Shugaban Amurka Donald Trump na yunkurin sauya sunan yankin tekun Fasha.

Ta jaddada cewa “wadanda ke neman canza sunan Tekun Fasha ba su fahimci tarihin dubban shekaru na Iran ba.”

Malama Mohajerani ta rubuta a dandalin na X cewa: Tekun Fasha bai takaita da kasancewa sunan yanki kadai ba, a’a ya zama wani muhimmin bangare na tarihin al’ummar Iran.

Ta kara da cewa: “Wadanda ke neman canza sunan ‘Tekun Fasha’ ba su fahimci tarihin Iran na dubban shekaru ba. Wannan yunkuri na nuna rashin sanin gaskiya da tarihi kafin ya zama batun neman tunzura Iran.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Kakabawa JMI Sabbin Takunkuman Tattalin A Jiya Alhamis

Gwamnatin kasar Amurka ta dorawa JMI sabbin takunkuman tattalin arziki ta bangaren man fetur a jiya Alhamis, a dai-dai lokacinda take maganar sake farfado tattaunawa da ita.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto  Scott Bessent sakataren kudi na Amurka yana fadar haka ‘Amurka zata ci gaba da gurgunta tattalin arzikin JMI da dukkan hanyoyin samun kudadenta, har sai ta dawo kan muradunta.

Wannan dai yana daga cikin shirin Amurka na takurawa tattalin arzikin kasar Iran har zuwa lokacinda mutanen kasar zasu kasa hakuri su kuma tashi su kifar da gwamnatin JMI daga cikin gida.

Wannan ne takunkuman tattalin arziki na farko wanda gwamnatin Amurkan ta dorawa JMI bayan yakin kwanaki 12 da ita da HKI suka dorawa kasar.

Takunkuman a halin yanzu ta shafi jami’an gwamnati 7 da kuma wani kamfani mai zaman kansa. Wannan dai yana nuna irin tsarin tupka da warwaran da gwamnatin Amurka take kai, tana neman sake farfado da tattaunawa da kuma kara takurawa kasar Iran a dayan bangaren.

Har’ila yau bayan yakin kwanaki 12 yana cewa ya amince China ta ci gaba da sayan man fetur na kasar Iran.

Wannan dais hi ne takunkuman tattalin arziki na 8 kan abinda ya shafi man fetur wanda gwamnatin Amurka ta dorawa Iran tun bayan dawowansa kan white a farkon wannan shekarar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Iran ta Bukaci Gudanar da Bincike Kan Sacewar jami’ar Diblomasiyyar kasar A Lebanon Shekaru 43 Da Suka gabata
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Ayatullahi Khatami Ya Ce Hukuncin Da Ya Cancanci Trump Da Netanyahu Shi Ne Kisa Saboda Zubar Da Jinin Bil’Adama
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC
  • Amurka Ta Kakabawa JMI Sabbin Takunkuman Tattalin A Jiya Alhamis
  • Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC
  • ‘Yan Nijeriya Na Kewar Gwamnatin Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi