Aminiya:
2025-05-22@15:42:01 GMT

ACF ta nemi Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen kisan jama’a a Filato

Published: 7th, April 2025 GMT

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa wajen kawo ƙarshen hare-haren da ake kai wa al’umma a Jihar Filato.

Ƙungiyar ta bayyana baƙin cikinta matuƙa kan harin da aka kai yankin Bokkos da Mangu a ranar 28 ga watan Maris, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama ciki har da ƙananan yara.

’Yan sanda sun soke gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Farfesa T.A. Muhammad-Baba ya fitar, ACF ta yi tir da waɗannan hare-hare tare da miƙa sakon ta’aziyyarta ga iyalan waɗanda suka rasu da kuma ɗaukacin jama’ar Jihar Filato.

Ƙungiyar ta ce hare-haren na ƙara jefa yankin Arewa cikin mawuyacin hali na rashin tsaro.

ACF ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ayyana dokar ta-ɓaci a wuraren da ake fama da hare-haren ‘yan bindiga tare da haɗa kai da al’ummomin yankin domin daƙile barazanar tsaro.

Haka kuma, ƙungiyar ta nemi gwamnati ta ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma kama waɗanda ke da hannu a ta’asar.

Ƙungiyar ta jaddada buƙatar wanzar da zaman lafiya a Jihar Filato tare da buƙatar a haɗa kai da shugabannin gargajiya, dattawa, ƙungiyoyi da sauran masu ruwa da tsaki domin daƙile lamarin.

ACF ta kuma bukaci al’umma su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai kan duk wani abu da ka iya kawo matsala.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Gwamnatin tarayya hare hare kungiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Nasarorin Noma da Tsaron Abinci Karkashin Shirin Renewed Hope
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Turawa ‘Yan Kasar Fararen Fata
  • Rukunin Karshe Na Alhazan Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
  • Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Jaddada Shirinta Na Yaki Da  Matsalar Tsaro 
  • An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato
  • Yeman ta yi barazanar killace tashar jiragen ruwan Haifa ta Isra’ila
  • Kwamishina ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe
  • Kwamishiniya ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe