Southampton Ta Koma Rukunin Ƴan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Tottenham
Published: 6th, April 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon kafa ta Southampton ba za ta buga gasar Firimiya Lig na badi ba, bayan da su ka koma gasar yan dagaji ta kasar Ingila, Southampton ta yi rashin nasara a hannun Tottenham Hotspur wanda kuma shi ne ya yi sanadiyar da Southampton ta koma gasar Championship ta kasar Ingila.
Hakan ya sa ta kasance kungiya ta farko a tarihin gasar da ta koma baya (relegation) bayan buga wasanni 31 kacal, Southampton ta samu maki 10 a wasanni 31 an zura mata kwallaye 74 a raga sannan kuma ta zura kwallaye 23 kacal a bana.
Ramsdale tsohon mai tsaron ragar Arsenal, ya taka rawar gani a wasan inda ya tare kwallayen da ka iya shiga raga har sau biyar a wasan, ciki har da kwallayen da Spence da Dominic Solanke su ka buga cikin kwarewa da zafin nama, amma kuma bakin sun rasa damarsu a lokacin da Tel ya ci wani bugun daga kai sai mai tsaron raga, biyo bayan keta da Welington ya yi a kan Johnson.
Bayar da damarmakin da Southampton ta yi wani abu ne da ya ci mata tuwo a kwarya, hakan ya sa ta zama kulob din da aka fi zurawa kwallo a raga inda aka zura mata kwallo 74 a wasanni 31 da su ka buga, kuma abu ne da za su magance idan har su na son dawowa gasar Firimiya a kakar wasa mai zuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila
এছাড়াও পড়ুন:
Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a Ilori
Hukumar Binciken Tsaro ta Najeriya (NSIB) ta sanar cewa mutanen da suka tsallake rijiya da baya a hatsarin jirgin sama da ya auku a Jihar Kwara suna samun kulawa a asibiti
Da yake tabbatar da cewe duka mutanen cikin jirgin horon sun tsira da ransu, Babban Daraktan NSIB, Kyaftin Alex Badeh Junior, ya ce hukumar ta gano katin nadar bayanai daga jirgin, bayan aukuwar hatsarin a filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilorin,
Jirgin, nau’in Diamond, mai lamba BNI, mallakin Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama ta Ilorin (IAC) ne, kuma ya yi hatsarin ne a yayin atisayen sauka na gwaji, inda ya kauce daga titi, ya yi cikin daji ya lalace fiye da yadda za a iya gyarawa.
Kyaftin Badeh ya bayyana Ya ce wadanda ya yi hatsari da su sun hada da shugaban horo, wanda aka sani da Ajape, da wata daliba, Lola. Dayansu ya samu rauni mai tsanani, ɗayan kuma ya samu raunuka marasa yawa, kuma dukansu suna karbar magani a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH).
Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma Za mu gina mayankar dabbobi a kan Naira biliyan 3 a Gombe —GwamnatiYa bayyana cewa ana nazarin katin bayanan da aka gano a dakin gwaje-gwajen NSIB, kuma ana sa ran za a fitar da rahoton farko cikin kwanaki 30 masu zuwa.
Ya jaddada cewa aikin hukumar shi ne gano abin da ya faru da kuma yadda za a hana sake faruwar irinsa a nan gaba, yana mai tabbatar wa jama’a cewa duk da hatsarin da ya faru, sararin samaniyar Najeriya yana nan cikin aminci.