Hamas ta ɗora alhakin harin da Isra’ila ta kai a kan Amurka
Published: 18th, March 2025 GMT
Ƙungiyar Hamas ta ɗora alhakin hare-haren da Isra’ila ta ƙaddamar yau Talata a Zirin Gaza kan Amurka.
A wata sabuwar sanarwa da Hamas ta fitar, ta ce Amurka ce ke da “alhakin kisan gillar” da aka yi a Gaza bayan da ta bayyana cewa Isra’ila ta shaida wa Amurka shirinta na kai hare-haren gabanin kai harin.
Sanarwar ta ce hakan ya “tona asirin ƙaryar da suke yi na iƙirarinsu kan damuwa da kawo ƙarshen yaƙin.
“Muna buƙatar ƙasashen duniya su ɗauki matakin gaggawa na kama masu aikata laifukan yaƙi da masu goya musu baya,” in ji Hamas.
A gefe guda kuma kafar yaɗa labarai da ke da alaƙa da Hamas, mai suna Filastin, ta ce an kashe jami’an gwamnatin Hamas huɗu a hare-haren Isra’ila.
Hazalika, shugaban hukumar lafiya da Hamas ke jagoranta, Munir al-Barsh ya ce mutane fiye da 660 aka jikkata a hare-haren, kuma wasu da dama na ƙarƙashin ɓaraguzai.
Majiyoyin kiwon lafiyar Gaza sun shaida wa gidan Talabijin na Al Jazeera cewa fiye da mutane 400 ne aka kashe, kuma mafi yawancinsu mata da ƙananan yara da kuma dattawa.
Harin wanda ke nuna kawo ƙarshen yarjejeniyar zaman lafiyar da aka ƙulla tsakanin Isra’ila da Hamas a watan Janairu, Isra’ila ta ce ta ƙaddamar da shi ne bayan da Hamas ta ƙi sako ragowar mutanen da ta yi garkuwa da su.
Wani jami’in Isra’ila ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP cewa, za su ci gaba ta kai hare-hare har sai sun kawar da shugabannin Hamas da gine-ginensu da kuma kayan aikinsu.
Fadar White House ta bakin sakatariyar yaɗa labaranta Karoline Leavitt, ta ce sai da Isra’ila ta sanar da ita, kafin ɗaukar matakin kai harin.
“Isra’ila ta sanar da gwamnatin Trump da fadar White House kan harin da suka kai Gaza a daren yau, kamar yadda shugaba Trump ya bayyana Hamas da Houthis da kuma Iran, da ke neman addabar Isra’ila har ma da Amurka, za su ɗanɗana kuɗarsu.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mafarauta 10 a Adamawa
Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.
Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalA cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.
Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.
“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.
Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.
“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”
Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.
Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.